ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya na musabiha da sababbin kwamishinonin zaɓen da aka rantsar

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya na musabiha da sababbin kwamishinonin zaɓen da aka rantsar

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gudanar da ganawa da manyan masu ruwa da tsaki a cikin harkokin zabe, kamar su jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen hula da kuma manema labarai kan sabon yunkurin shirye-shiryen zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo.

Wannan ita ce ganawa irinta ta farko tun bayan kammala zaben cike gurbi da ya gudana a watan Fabrairun 2024, a jihohi 26 da ke fadin kasar nan.

Babban makasudin taron shi ne, yadda za a samu nasarar gudanar da sahihin zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo. Zaben gwamnan Jihar Edo zai gudana ne a ranar 21 ga Satumbar 2024, yayin da za a yi zaben gwamnan Jihar Ondo a ranar Asabar, 16 ga Nuwambar 2024.

ADVERTISEMENT

Tuni dai jam’iyyu suka gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnan Jihar Edo. A cewar jadawalin zaben, jam’iyyu suna da kwanaki 21 ne kacal wajen mika bayanan ‘yan takararsu ga hukumar zabe.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya jagoranci ganawar ya bayyana cewa hukumarsa ta horar da jami’an jam’iyyu na yankuna ta yadda za a taimaka wa dukkan jam’iyyun siyasan. Ya kara da cewa sun bude adireshin amsar bayanan ne tun a ranar 4 ga Maris, 2024, sannan kuma suka rufe da misalin karfe 6 na yamma na ranar Asabar, 24 ga Maris ta 2024.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

A cewarsa, bayan makonni biyu aka sake budewa saboda ba dukkan jam’iyyu suka saka bayyana ‘yan takaransu ba.

Hukumar INEC ta yi kira ga jam’iyyun siyasa su ci gaba da bin jaddawalin ayyukan zaben domin kaucewa rudadi.

Za dai a fara gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnan Jihar Ondo a ranar 6 ga Afrilun 2024, wanda za a kammala a ranar 27 ga Afrilun 2024. A ciki jam’iyyun siyasa 19, 16 ne kadai suka nuna sha’awarsu ta shiga zaben.

Da yake jawabi, shugaban gamayyar jam’iyyu, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa babu uzuri matukar an gaza gudanar da zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo yadda ya kamata.

Jihohin Edo da Ondo dai kowannensu yana da kananan hukumomin 18. Yayin da Jihar Edo take da masu rajistar zabe guda 2,501,081, cibiyoyin zabe 192 da kuma rumfunan zabe 4,519, inda Jihar Ondo take da yawan masu rajistar zabe guda 1,991,344, cibiyoyin zabe 203 da kuma rumfunan zabe 3,933.

zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
bashi

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.