ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar PDP na yankin arewa ta tsakiya ta fara tattaunawa da shugabannin jam’iyyar PDP domin fitar da shugaban jam’iyyar na kasa daga yanki domin samun damar kammala wa’adin mulkin Dakta Iyorchia Ayu.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar ta sanar da ranar gudanar da babban taron kwamitin zartarwa da ta tsara za a yi a ranakun 17 da 18 ga Afrilun 2024.

  • An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19
  • Bayani A Kan Zakkar Shan Ruwa Da Sallar Idi

Rahotanni sun bayyana cewa tattaunawar a tsakanin shugabanni jam’iyyar a yankin ya yi nisa.
Wata majiya mai tushe ta ce, “Muna tsammanin yankin zai bayyana zabinsa kafin babban taron kwamitin zartarwa.”

ADVERTISEMENT

Cikin mutanen da ake tsammanin za a fitar sun hada da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki daga Jihar Kwara da Sanata Gabriel Suswam wanda suka fito daga wuri daya da Ayu a Jihar Benuwai.
Haka kuma an bayyana cewa shugabannin jam’iyyar a yankin sun gana a Abuja domin gudanar da shirye-shiryen cimma wannan burin nasu.

Wadanda suka halarci ganawar sun hada da shugabannin jam’iyyar na jihohi shida da ke yankin arewa ta tsakiya ciki har da na Abuja da kuma sauran wakilai da aka zaba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Sakamakon ganawar ya nuna cewa mahalarta tron sun amince shugabancin PDP ya tsaya a yankin arewa ta tsakiya domin kammala wa’adin mulkin Ayu, yayin mafi yawanci suka amince da cewa Damagum ya ci gaba da rike mukaminsa na mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa.

Majiya a wurin taron ta bayyana cewa ana tsammanin gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang zai shirya taron shugabannin yankin domin tattauna yadda za a cimma samun wannan nasara.

Majiyar ta ce, “Da yake yanzu zaben 2023 ya shude, muna tsammanin shugabannin jam’iyyar za su yi abin da ya dace wajen sake fasalin jam’iyyarmu dpmin ta dawo kan hayyacinta.

“Lokacin da Ayu yake shugabancin jam’iyyar ya yi kokari sosai, shi ya sa mu mutanen yankin arewa na tsakiya muka hadu wuri guda tare da amincewa a maye gurbinsa daga cikinmu, saboda matsayar da aka cimma a 2023 har yanzu tana aiki. Tsarin mulkin jam’iyyarmu ya amince da haka.

“Mun gudanar da taro kan wannan matsalar. Idan za mu iya tunawa dai, shugabanninmu sun gudanar da ganawa a Abuja, bayan taron kwamitin gudanarwa na jam’iyyar.”

A dai mika shugabancin jam’iyyar PDP a yankin arewa ta tsakiya kafin zaben 2023, wanda Ayu ya zama shugabanta ba tare da wata hamayyya ba.

An dai zabi Ayu ne domin ya maye gurbin Prince Uche Secondus wanda aka cire daga mukaminsa bisa rawar da mai gidansa a siyasa ya taka kan lamarin.

Ya dai fuskanci matsin lamba daga wurin Wike Nyesom Wike shugaban gwamnonin PDP biyar da suka balle da ake kira G-5, tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya lashe zaben fitar da gwani na neman tikitin zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.

Bayan samun takaddama mai zafi, daga karshe dai an cire Ayu a matsayin shugaban PDP, inda aka sa mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin arewa, Illiya Damagum dan asalin Jihar Yobe da ke yankin arewa maso gabas a matsayin mukaddashin shugaba tun daga ranar 28 ga Maris na 2023.

A yanzu haka dai kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da Damagum yake jagoranta yana shan matsin lamba kan gudanar da babban taron jam’iyyar na kasa.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.