ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar PDP na yankin arewa ta tsakiya ta fara tattaunawa da shugabannin jam’iyyar PDP domin fitar da shugaban jam’iyyar na kasa daga yanki domin samun damar kammala wa’adin mulkin Dakta Iyorchia Ayu.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar ta sanar da ranar gudanar da babban taron kwamitin zartarwa da ta tsara za a yi a ranakun 17 da 18 ga Afrilun 2024.

  • An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19
  • Bayani A Kan Zakkar Shan Ruwa Da Sallar Idi

Rahotanni sun bayyana cewa tattaunawar a tsakanin shugabanni jam’iyyar a yankin ya yi nisa.
Wata majiya mai tushe ta ce, “Muna tsammanin yankin zai bayyana zabinsa kafin babban taron kwamitin zartarwa.”

ADVERTISEMENT

Cikin mutanen da ake tsammanin za a fitar sun hada da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki daga Jihar Kwara da Sanata Gabriel Suswam wanda suka fito daga wuri daya da Ayu a Jihar Benuwai.
Haka kuma an bayyana cewa shugabannin jam’iyyar a yankin sun gana a Abuja domin gudanar da shirye-shiryen cimma wannan burin nasu.

Wadanda suka halarci ganawar sun hada da shugabannin jam’iyyar na jihohi shida da ke yankin arewa ta tsakiya ciki har da na Abuja da kuma sauran wakilai da aka zaba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Sakamakon ganawar ya nuna cewa mahalarta tron sun amince shugabancin PDP ya tsaya a yankin arewa ta tsakiya domin kammala wa’adin mulkin Ayu, yayin mafi yawanci suka amince da cewa Damagum ya ci gaba da rike mukaminsa na mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa.

Majiya a wurin taron ta bayyana cewa ana tsammanin gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang zai shirya taron shugabannin yankin domin tattauna yadda za a cimma samun wannan nasara.

Majiyar ta ce, “Da yake yanzu zaben 2023 ya shude, muna tsammanin shugabannin jam’iyyar za su yi abin da ya dace wajen sake fasalin jam’iyyarmu dpmin ta dawo kan hayyacinta.

“Lokacin da Ayu yake shugabancin jam’iyyar ya yi kokari sosai, shi ya sa mu mutanen yankin arewa na tsakiya muka hadu wuri guda tare da amincewa a maye gurbinsa daga cikinmu, saboda matsayar da aka cimma a 2023 har yanzu tana aiki. Tsarin mulkin jam’iyyarmu ya amince da haka.

“Mun gudanar da taro kan wannan matsalar. Idan za mu iya tunawa dai, shugabanninmu sun gudanar da ganawa a Abuja, bayan taron kwamitin gudanarwa na jam’iyyar.”

A dai mika shugabancin jam’iyyar PDP a yankin arewa ta tsakiya kafin zaben 2023, wanda Ayu ya zama shugabanta ba tare da wata hamayyya ba.

An dai zabi Ayu ne domin ya maye gurbin Prince Uche Secondus wanda aka cire daga mukaminsa bisa rawar da mai gidansa a siyasa ya taka kan lamarin.

Ya dai fuskanci matsin lamba daga wurin Wike Nyesom Wike shugaban gwamnonin PDP biyar da suka balle da ake kira G-5, tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya lashe zaben fitar da gwani na neman tikitin zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.

Bayan samun takaddama mai zafi, daga karshe dai an cire Ayu a matsayin shugaban PDP, inda aka sa mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin arewa, Illiya Damagum dan asalin Jihar Yobe da ke yankin arewa maso gabas a matsayin mukaddashin shugaba tun daga ranar 28 ga Maris na 2023.

A yanzu haka dai kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da Damagum yake jagoranta yana shan matsin lamba kan gudanar da babban taron jam’iyyar na kasa.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

PDP
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.