• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabar NIS Ta Ziyarci Jami’an Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Sakkwato

by Sadiq
2 years ago
NIS

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Shige Da Fice ta Kasa (NIS), Wuraola Adepoju, ta tabbatar da goyon bayanta ga iyalan jami’an hukumar da ‘yan bindiga suka kai wa hari a kan iyakar Ilela da ke Jihar Sakkwato.

‘Yan bindigar sun kashe jami’an hukumar biyu tare da raunata wasu hudu.

  • Manchester United Ta Cimma Yarjejeniya Da West Ham A Kan Maguire
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Janye Zanga-zangar Da Suka Shirya

Hakan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ta bayyana cewa hukumar za ta kula da kudaden jinyar jami’an da suka samu rauni, kamar yadda wata sanarwa da kakakin hukumar, Dakta Dotun Aridegbe ya fitar.

Harin dai ya faru ne a wani shingen bincike da ke unguwar Gwadabawa a Jihar Sakkwato a karshen watan Yuli.

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun kai hari shingen binciken da ke kauyen Mamman Suka a karamar hukumar Gwadabawa, inda suka kashe jami’ai biyu tare da raunata wasu hudu wanda daga bisani aka garzaya da su asibitin koyarwa na Jami’ar Usman Danfodiyo, da ke Sakkwato.

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

NIS

Mukaddashiyar ta nuna alhininta game da lamarin, inda ta jinjina wa kwazon jami’an da suka yi artabu da maharan.

Har wa yau, ta kuma jajanta wa iyalan jami’an da suka rasu, inda ta tabbatar musu da cewa hidimar da suka yi wa kasa ba za ta tashi a banza ba.

Mukaddashiyar wadda a baya ta kai ziyarar ban girma ga gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Aliyu Sakkwato, ta bayyana shirin hukumar na gudanar da ayyuka ba tare da la’akari da kalubalen da suke fuskanta ba.

Ta kuma bai wa gwamnan tabbacin cewa NIS za ta ci gaba da kula da iyakokin kasar nan tare da samar da dabarun dakile kwararar bakin haure.

Ta samu rakiyar shugaban hukumar NIS na Jihar Sakkwato da kuma takwaransa na babban birnin tarayya, Kwanturola Tony Akuneme.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

'Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.