ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabar NIS Ta Ziyarci Jami’an Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Sakkwato

by Sadiq
3 years ago
NIS

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Shige Da Fice ta Kasa (NIS), Wuraola Adepoju, ta tabbatar da goyon bayanta ga iyalan jami’an hukumar da ‘yan bindiga suka kai wa hari a kan iyakar Ilela da ke Jihar Sakkwato.

‘Yan bindigar sun kashe jami’an hukumar biyu tare da raunata wasu hudu.

  • Manchester United Ta Cimma Yarjejeniya Da West Ham A Kan Maguire
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Sun Janye Zanga-zangar Da Suka Shirya

Hakan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ta bayyana cewa hukumar za ta kula da kudaden jinyar jami’an da suka samu rauni, kamar yadda wata sanarwa da kakakin hukumar, Dakta Dotun Aridegbe ya fitar.

ADVERTISEMENT

Harin dai ya faru ne a wani shingen bincike da ke unguwar Gwadabawa a Jihar Sakkwato a karshen watan Yuli.

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun kai hari shingen binciken da ke kauyen Mamman Suka a karamar hukumar Gwadabawa, inda suka kashe jami’ai biyu tare da raunata wasu hudu wanda daga bisani aka garzaya da su asibitin koyarwa na Jami’ar Usman Danfodiyo, da ke Sakkwato.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

NIS

Mukaddashiyar ta nuna alhininta game da lamarin, inda ta jinjina wa kwazon jami’an da suka yi artabu da maharan.

Har wa yau, ta kuma jajanta wa iyalan jami’an da suka rasu, inda ta tabbatar musu da cewa hidimar da suka yi wa kasa ba za ta tashi a banza ba.

Mukaddashiyar wadda a baya ta kai ziyarar ban girma ga gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Aliyu Sakkwato, ta bayyana shirin hukumar na gudanar da ayyuka ba tare da la’akari da kalubalen da suke fuskanta ba.

Ta kuma bai wa gwamnan tabbacin cewa NIS za ta ci gaba da kula da iyakokin kasar nan tare da samar da dabarun dakile kwararar bakin haure.

Ta samu rakiyar shugaban hukumar NIS na Jihar Sakkwato da kuma takwaransa na babban birnin tarayya, Kwanturola Tony Akuneme.

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

'Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.