ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Amurka Ta Sake Yada Karairayi Ta Hanyar Zargin Sin Da Tallafawa Rasha Da Makamai

by CGTN Hausa
1 year ago
Sin

Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Geng Shuang, ya zargi Amurka da yada karairayi, cewa wai kasar Sin na taimakawa Rasha da makamai a rikicin ta da Ukraine.

Geng Shuang, wanda ya yi tsokacin a jiya Juma’a, yayin zaman kwamitin tsaron MDD da aka yi, don nazartar batutuwan da suka shafi tallafin makamai ga Ukraine, inda ya ce ko kadan Sin ba za ta amince da wannan zargi ba.

  • Sin: A Bara Darajar Cinikayya Tsakanin Kasashen Shiyya Karkashin RCEP Ta Kai Dala Triliyan 5.6
  • Mataimakin Shugaban Brazil: Sin Ta Nuna Babban Misali A Fannin Yaki Da Fatara Da Bunkasa Fasahohi

Geng Shuang ya kuma jaddada cewa, ba Sin ce ta kirkiri rikicin Ukraine ba, kuma ba ta da hannu cikin gudanar sa. Har kullum Sin na nacewa manufar shawo kan rikicin ta hanyar siyasa, da kayyade dukkanin kayayyakin aikin soji da ake iya amfani da su a harkokin fararen hula, kuma ko kadan Sin ba ta samar da makamai ga ko wane bangare na rikicin.

ADVERTISEMENT

Jami’in ya kara da cewa, dukkanin harkokin raya tattalin arziki da cinikayya dake gudana tsakanin Sin da Rasha, ana gudanar da su ne bisa ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, da sauran tsare tsaren kasuwanni, kuma ba su da wata manufa ta illata wani sashe na daban, ko karya dokokin kasa da kasa.

Hasali ma a cewar jami’in, bayan barkewar rikicin Rasha da Ukraine, ba a taba dakatar da hada hadar cinikayya tsakanin Amurka da Rasha ba. Sai dai abun takaici a irin wannan yanayi, Amurka na ci gaba da zargin kasar Sin kan halastattun huldodin cinikayyar ta da Rasha, kawai da nufin kawar da zargi daga kan ta, da kaucewa daukar alhakin laifin ta.

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Daga nan sai Geng Shuang ya ce Sin na kira ga Amurka, da ta dakatar da batawa Sin suna ta fakewa da batun Ukraine, ta dakatar da kakaba takunkumai na kashin kai, da kokarin murkushe kamfanonin Sin. Ya ce har kullum, Sin na fatan Amurka za ta yi kokarin ba da kyakkyawar gudumawa, wajen ganin an kawo karshen yaki, da maido da zaman lafiya cikin hanzari. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
Daga Birnin Sin

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Next Post
Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi

Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.