ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Saurayinta

Jami’an rundunar ‘yansanda a Jihar Imo sun kama wata mata ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi bisa zarginta da daba wa saurayinta, Kelechi Nzemechi, wuka har lahira sakamakon wata rigima da ta kaure tsakaninsu a kan kin ba ta kasonta na kudin da suka yi damfara ta intanet.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yansandan Jihar, Henry Okoye, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a Owerri a lokacin da yake gabatar da wacce ake zargin, ya ce Oluchi ta amsa laifin kashe saurayin nata ne kan kin ba ta kaso daga sama da kudin kasar Indonesiya miliyan 250 da suka damfari wani mutum dan kasar.

  • Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

Da take bayar da labarin mummunan al’amarin, rundunar ‘yansandan ta bayyana cewa wacce ake zargin ta yi ikirarin cewa saurayin nata da ta kashe ya gabatar da ita ga wanda za su damfara har ta kai ga sun samu wadannan kudade, inda ta kara da cewa ta yi amfani da wuka a kicin wajen daba masa wuka bayan da suka yi zazzafar gardama.

ADVERTISEMENT

“Rundunar ‘yansandan ta gudanar da bincike mai zurfi sun cafke wata budurwa ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi da ke unguwar Uzoagba a Karamar Hukumar Ikeduru ta Jihar Imo da laifin daba wa abokin aikinta, Kelechi Nzemechi, mai shekaru 31 wuka wanda ya kai shi ga mutuwa.

“Yayin da take amsa tambaya, wacce ake zargin ta amsa laifinta, ta yarda cewa masoyinta ne ya yaudare ta inda ya jefa hanyar damfarar intanet mai suna ‘yahoo yahoo’.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A ranar 02/06/2024, ta yi zazzafar husuma da shi saboda ya kasa ba ta wani kaso na kudin da ake zargin ta kai Rupiah Miliyan 250 da suka samu daga hannun wani da suka damfara a Indonesia, inda daga nan ne ta yi amfani da wukar kicin ta daba masa wuka a wani bangare na jikinsa,” in ji ‘yan sanda.

A lokacin da take zantawa da ‘yan jarida, Oluchi ta bayyana yadda ta yi kokarin wanke kanta daga kashe shi ta hanyar rubuta wasikar yaudara, “A kokarin da na ke na boye laifina, na yi gaggawar rubutawa a takarda; ‘Kana tunanin za ka ci kudina ka tafi haka, ni uwa ce ga samari, ina zuwa don neman matarka da yaronka har da danginka. Sai na dora takardar a kan gawar sannan na gudu daga gidan,” in ji ta.

Wacce ake zargin ta kuma bayyana cewa tana zaune da wanda ta kashe tun shekarar 2019 inda suka haifi yaro tare. ASP Okoye ya ce za a gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Saurayinta
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.