ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Saurayinta

Jami’an rundunar ‘yansanda a Jihar Imo sun kama wata mata ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi bisa zarginta da daba wa saurayinta, Kelechi Nzemechi, wuka har lahira sakamakon wata rigima da ta kaure tsakaninsu a kan kin ba ta kasonta na kudin da suka yi damfara ta intanet.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yansandan Jihar, Henry Okoye, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a Owerri a lokacin da yake gabatar da wacce ake zargin, ya ce Oluchi ta amsa laifin kashe saurayin nata ne kan kin ba ta kaso daga sama da kudin kasar Indonesiya miliyan 250 da suka damfari wani mutum dan kasar.

  • Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

Da take bayar da labarin mummunan al’amarin, rundunar ‘yansandan ta bayyana cewa wacce ake zargin ta yi ikirarin cewa saurayin nata da ta kashe ya gabatar da ita ga wanda za su damfara har ta kai ga sun samu wadannan kudade, inda ta kara da cewa ta yi amfani da wuka a kicin wajen daba masa wuka bayan da suka yi zazzafar gardama.

ADVERTISEMENT

“Rundunar ‘yansandan ta gudanar da bincike mai zurfi sun cafke wata budurwa ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi da ke unguwar Uzoagba a Karamar Hukumar Ikeduru ta Jihar Imo da laifin daba wa abokin aikinta, Kelechi Nzemechi, mai shekaru 31 wuka wanda ya kai shi ga mutuwa.

“Yayin da take amsa tambaya, wacce ake zargin ta amsa laifinta, ta yarda cewa masoyinta ne ya yaudare ta inda ya jefa hanyar damfarar intanet mai suna ‘yahoo yahoo’.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A ranar 02/06/2024, ta yi zazzafar husuma da shi saboda ya kasa ba ta wani kaso na kudin da ake zargin ta kai Rupiah Miliyan 250 da suka samu daga hannun wani da suka damfara a Indonesia, inda daga nan ne ta yi amfani da wukar kicin ta daba masa wuka a wani bangare na jikinsa,” in ji ‘yan sanda.

A lokacin da take zantawa da ‘yan jarida, Oluchi ta bayyana yadda ta yi kokarin wanke kanta daga kashe shi ta hanyar rubuta wasikar yaudara, “A kokarin da na ke na boye laifina, na yi gaggawar rubutawa a takarda; ‘Kana tunanin za ka ci kudina ka tafi haka, ni uwa ce ga samari, ina zuwa don neman matarka da yaronka har da danginka. Sai na dora takardar a kan gawar sannan na gudu daga gidan,” in ji ta.

Wacce ake zargin ta kuma bayyana cewa tana zaune da wanda ta kashe tun shekarar 2019 inda suka haifi yaro tare. ASP Okoye ya ce za a gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Saurayinta
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.