• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: An Fitar Da Shirin Gaggauta Gina Ingantaccen Tsarin Ayyukan Lissafin Na’urori Masu Kwakwalwa Mai Karfi Na Kasa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin: An Fitar Da Shirin Gaggauta Gina Ingantaccen Tsarin Ayyukan Lissafin Na’urori Masu Kwakwalwa Mai Karfi Na Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta fitar da shirin gaggauta gina ingantaccen tsarin ayyukan lissafin na’urori masu kwakwalwa mai karfi na kasa, wanda zai hade damar samar da hidimomin manyan lissafi daga na’urori masu kwakwalwa.

Shirin zai ingiza aiwatar da tsarin kasar na “Tattara bayanai daga gabas da tasaftawa a yammacin kasa”, da gaggauta gina hadakar na’urori masu kwakwalwa masu matukar karfin sarrafa bayanai na kasa.

  • Jirgin Ruwa Mai Binciken Teku Na Farko Na Kasar Sin Ya Gwada Yin Aiki Cikin Nasara
  • Sin Ta yi Nasarar Harba Tare Da Gwada Taurarin Dan Adam Na C Karo Na 24

Shirin wanda hukumomin kasar 5 suka fitar, ciki har da hukumar kula da bayanan kwamfuta ta kasar da kwamitin tsara manufofin samar da ci gaba da aiwatar da sauye sauye na kasar, na da nufin zaburar da ci gaban tattalin arzikin kasa mai kunshe da managarcin karfin ayyukan na’urori masu kwakwalwa, ta yadda hakan zai ba da gagarumar gudummawa ta gina karfin kasar a fannin tsaron yanar gizo, da tattalin arziki na dijital.

Shirin ya yi hasashen cewa, ya zuwa karshen shekarar 2025, Sin za ta samar da cikakken tsarin ayyukan ababen more rayuwa masu nasaba da na’urori masu kwakwalwa mafiya karfin lissafi. Kana adadin sabon mizanin karfin lissafin na’urori masu kwakwalwa na kasar zai zarce kaso 60 bisa dari, kuma karfin ayyukansu zai samar da sauki da rahusa, yayin da fasahohin da ake bukata domin cin gajiya daga hakan za su kasance masu tsaro da inganci.

Bugu da kari, shirin ya tanadi gudanar da ayyukan tsara karfin lissafin na’urori masu kwakwalwa tsakanin gabashi da tsakiya da yammacin kasar Sin, tare da yayata hade gajiyar karfin lissafin na’urorin, da bayanai da tsarin ayyukan manhajoji. Har ila yau, za a tsara da bunkasa, da wanzar da tsaron karfin aikin na’urori masu kwakwalwa yadda ya kamata. (Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kashe Wasu Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane 6, Sun Kwato Kudade A Bauchi 

Next Post

Ci Gaba Da Gudanar Da Sha’Anin Da Mao Zedong Ya Kaddamar, Shi Ne Abu Mafi Dacewa Game Da Tunawa Da Shi

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Ci Gaba Da Gudanar Da Sha’Anin Da Mao Zedong Ya Kaddamar, Shi Ne Abu Mafi Dacewa Game Da Tunawa Da Shi

Ci Gaba Da Gudanar Da Sha’Anin Da Mao Zedong Ya Kaddamar, Shi Ne Abu Mafi Dacewa Game Da Tunawa Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.