Hukumar kula da gina unguwanni ta kasar Masar da wani kamfanin hadin gwiwa na Sin da Masar, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar kafawa da kula da cibiyar harkokin kasuwanci (CBD), ta sabon birnin harkokin mulki na kasar Masar.
Bisa yarjejeniyar, kamfanin Horizon Operation Management na kasar Masar wanda a baya ke kula da kadarori da harkokin birnin, shi zai ja ragamar kula da aikin kafa cibiyar ta CBD.
Da yake jawabi gabanin rattaba hannu kan yarjejeniyar, ministan kula da gidaje na kasar Sherif El-Sherbiny ya sanar da cewa, yarjejeniyar ta shafi aikin kulawa da tafiyar da muhimman kayayyakin more rayuwa da hidimtawa mazauna da masu yawon bude ido da harkokin kasuwanci a cibiyar.
Ya kuma nanata cewa, yunkurin alama ce ta dabarar gwamnatin kasar ta sauyawa daga tsare-tsaren da aka saba da su a baya, zuwa mayar da hankali kan kula da kayayyakin al’umma da tsarin shugabanci mai gudanar da ayyuka da mayar da hankali kan inganci da dorewarsa. (Mai Fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp