ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

by Sulaiman
3 weeks ago
default

default

A bana ake cika shekaru 10 da kulla yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, inda duniya ta shiga wani sabon mataki dangane da jagorancin matakai da ake dauka na dakile kalubalen sauyin yanayi. Hakan ne ma ya sa a yayin taron MDD na sauyin yanayi karo na 30 da ya gudana a birnin Belem na kasar Brazil a baya bayan nan, aka dora muhimmancin gaske ga manyan batutuwan da suka shafi kana, inda aka karfafa kira ga sassan kasa da kasa da su yi aiki tare wajen lalubo dabarun magance sauyin yanayi, da gaggauta rage fitar da nau’o’in hayaki masu dumama yanayi, da matakan karfafa juriyar sassan kasa da kasa ga illolin sauyin yanayi, da ma ingiza tafiya tare, da kuma sauyi zuwa dabarun kyautata yanayi na bai daya.

Duk da koma baya daga wasu kasashen duniya game da nauyin da ya kamata su sauke a wannan tafiya, kasar Sin ta yi gaba wajen aiwatar da managartan manufofin jagoranci, da suka sanya ta a sahun gaba ta fuskar sauke nauyi da hakkin da ya rataya a wuyanta.

A matsayinta na babbar kasar mai hangen nesa da dattaku, Sin ta rungumi manufar kasancewar kasashe masu mabambantan tasiri a duniya, tana ta zurfafa hadin gwiwa, da aiki tukuru wajen gina tsarin cimma matsaya guda a fannin yaki da sauyin yanayi. Har ila yau, kasar Sin ta himmatu wajen ingiza matakan da suka dace duniya baki daya ta aiwatar, don shawo kan wannan kalubale na sauyin yanayi.

ADVERTISEMENT

Hakan zai fito fili idan muka waiwayi jawabin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gabatar shekaru goma da suka gabata, yayin taron sauyin yanayi na Paris. A lokacin ya yi kira da babbar murya da a yi amfani da yarjejeniyar wajen cimma nasarar tsare-tsaren aiki na MDD, da fayyace taswirar sauya tafiya zuwa dabarun ci gaba marasa gurbata yanayi da sai sauran matakai masu nasaba.

A cikin gida kuwa, Sin ta yi aiki mara iyaka, wajen tabbatar da ta bayar da isasshiyar gudummawar cimma burikan magance sauyin yanayi. Karkashin hakan a shekarar 2009, Sin ta sanar da burinta na rage fitar da hayakin carbon zuwa shekarar 2020 bisa radin kanta. Ta kuma cimma wannan buri kafin ma cikar wa’adin. Kazalika, a watan Yunin shekarar 2015, Sin ta sanar da takamainan matakanta na cimma nasarar yarjejeniyar Paris wato NDC zuwa shekarar 2030.

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Sin ba ta tsaya a nan ba, inda a watan Satumban bana, ta sake fitar da kudurorinta na NDC na nan zuwa shekarar 2035, masu kunshe da aniyar kara rage fitar da iskar carbon bisa babban matsayi, da fadada kudurori masu nasaba da hakan a dukkanin fannonin tattalin arzikin kasa.

Da wadannan matakai da ma wasu karin manufofin, Sin ta martaba aniyarta, ta kuma nuna matsayinta na babbar kasa mai tasowa, wadda duniya ke kara martabawa bisa nauyin da take saukewa ta hanyar aiwatar da matakai na zahiri, da hadin gwiwa tare da dukkanin sassa masu ruwa da tsaki, ta yadda duniya za ta kubuta daga mummunan tasirin sauyin yanayi, a kuma gudu tare a tsira tare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Next Post
Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.