ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

by Sulaiman
10 months ago
default

default

A bana ake cika shekaru 10 da kulla yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, inda duniya ta shiga wani sabon mataki dangane da jagorancin matakai da ake dauka na dakile kalubalen sauyin yanayi. Hakan ne ma ya sa a yayin taron MDD na sauyin yanayi karo na 30 da ya gudana a birnin Belem na kasar Brazil a baya bayan nan, aka dora muhimmancin gaske ga manyan batutuwan da suka shafi kana, inda aka karfafa kira ga sassan kasa da kasa da su yi aiki tare wajen lalubo dabarun magance sauyin yanayi, da gaggauta rage fitar da nau’o’in hayaki masu dumama yanayi, da matakan karfafa juriyar sassan kasa da kasa ga illolin sauyin yanayi, da ma ingiza tafiya tare, da kuma sauyi zuwa dabarun kyautata yanayi na bai daya.

Duk da koma baya daga wasu kasashen duniya game da nauyin da ya kamata su sauke a wannan tafiya, kasar Sin ta yi gaba wajen aiwatar da managartan manufofin jagoranci, da suka sanya ta a sahun gaba ta fuskar sauke nauyi da hakkin da ya rataya a wuyanta.

A matsayinta na babbar kasar mai hangen nesa da dattaku, Sin ta rungumi manufar kasancewar kasashe masu mabambantan tasiri a duniya, tana ta zurfafa hadin gwiwa, da aiki tukuru wajen gina tsarin cimma matsaya guda a fannin yaki da sauyin yanayi. Har ila yau, kasar Sin ta himmatu wajen ingiza matakan da suka dace duniya baki daya ta aiwatar, don shawo kan wannan kalubale na sauyin yanayi.

ADVERTISEMENT

Hakan zai fito fili idan muka waiwayi jawabin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gabatar shekaru goma da suka gabata, yayin taron sauyin yanayi na Paris. A lokacin ya yi kira da babbar murya da a yi amfani da yarjejeniyar wajen cimma nasarar tsare-tsaren aiki na MDD, da fayyace taswirar sauya tafiya zuwa dabarun ci gaba marasa gurbata yanayi da sai sauran matakai masu nasaba.

A cikin gida kuwa, Sin ta yi aiki mara iyaka, wajen tabbatar da ta bayar da isasshiyar gudummawar cimma burikan magance sauyin yanayi. Karkashin hakan a shekarar 2009, Sin ta sanar da burinta na rage fitar da hayakin carbon zuwa shekarar 2020 bisa radin kanta. Ta kuma cimma wannan buri kafin ma cikar wa’adin. Kazalika, a watan Yunin shekarar 2015, Sin ta sanar da takamainan matakanta na cimma nasarar yarjejeniyar Paris wato NDC zuwa shekarar 2030.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sin ba ta tsaya a nan ba, inda a watan Satumban bana, ta sake fitar da kudurorinta na NDC na nan zuwa shekarar 2035, masu kunshe da aniyar kara rage fitar da iskar carbon bisa babban matsayi, da fadada kudurori masu nasaba da hakan a dukkanin fannonin tattalin arzikin kasa.

Da wadannan matakai da ma wasu karin manufofin, Sin ta martaba aniyarta, ta kuma nuna matsayinta na babbar kasa mai tasowa, wadda duniya ke kara martabawa bisa nauyin da take saukewa ta hanyar aiwatar da matakai na zahiri, da hadin gwiwa tare da dukkanin sassa masu ruwa da tsaki, ta yadda duniya za ta kubuta daga mummunan tasirin sauyin yanayi, a kuma gudu tare a tsira tare.

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.