ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

by Sulaiman
7 months ago
default

default

A bana ake cika shekaru 10 da kulla yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, inda duniya ta shiga wani sabon mataki dangane da jagorancin matakai da ake dauka na dakile kalubalen sauyin yanayi. Hakan ne ma ya sa a yayin taron MDD na sauyin yanayi karo na 30 da ya gudana a birnin Belem na kasar Brazil a baya bayan nan, aka dora muhimmancin gaske ga manyan batutuwan da suka shafi kana, inda aka karfafa kira ga sassan kasa da kasa da su yi aiki tare wajen lalubo dabarun magance sauyin yanayi, da gaggauta rage fitar da nau’o’in hayaki masu dumama yanayi, da matakan karfafa juriyar sassan kasa da kasa ga illolin sauyin yanayi, da ma ingiza tafiya tare, da kuma sauyi zuwa dabarun kyautata yanayi na bai daya.

Duk da koma baya daga wasu kasashen duniya game da nauyin da ya kamata su sauke a wannan tafiya, kasar Sin ta yi gaba wajen aiwatar da managartan manufofin jagoranci, da suka sanya ta a sahun gaba ta fuskar sauke nauyi da hakkin da ya rataya a wuyanta.

A matsayinta na babbar kasar mai hangen nesa da dattaku, Sin ta rungumi manufar kasancewar kasashe masu mabambantan tasiri a duniya, tana ta zurfafa hadin gwiwa, da aiki tukuru wajen gina tsarin cimma matsaya guda a fannin yaki da sauyin yanayi. Har ila yau, kasar Sin ta himmatu wajen ingiza matakan da suka dace duniya baki daya ta aiwatar, don shawo kan wannan kalubale na sauyin yanayi.

ADVERTISEMENT

Hakan zai fito fili idan muka waiwayi jawabin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gabatar shekaru goma da suka gabata, yayin taron sauyin yanayi na Paris. A lokacin ya yi kira da babbar murya da a yi amfani da yarjejeniyar wajen cimma nasarar tsare-tsaren aiki na MDD, da fayyace taswirar sauya tafiya zuwa dabarun ci gaba marasa gurbata yanayi da sai sauran matakai masu nasaba.

A cikin gida kuwa, Sin ta yi aiki mara iyaka, wajen tabbatar da ta bayar da isasshiyar gudummawar cimma burikan magance sauyin yanayi. Karkashin hakan a shekarar 2009, Sin ta sanar da burinta na rage fitar da hayakin carbon zuwa shekarar 2020 bisa radin kanta. Ta kuma cimma wannan buri kafin ma cikar wa’adin. Kazalika, a watan Yunin shekarar 2015, Sin ta sanar da takamainan matakanta na cimma nasarar yarjejeniyar Paris wato NDC zuwa shekarar 2030.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Sin ba ta tsaya a nan ba, inda a watan Satumban bana, ta sake fitar da kudurorinta na NDC na nan zuwa shekarar 2035, masu kunshe da aniyar kara rage fitar da iskar carbon bisa babban matsayi, da fadada kudurori masu nasaba da hakan a dukkanin fannonin tattalin arzikin kasa.

Da wadannan matakai da ma wasu karin manufofin, Sin ta martaba aniyarta, ta kuma nuna matsayinta na babbar kasa mai tasowa, wadda duniya ke kara martabawa bisa nauyin da take saukewa ta hanyar aiwatar da matakai na zahiri, da hadin gwiwa tare da dukkanin sassa masu ruwa da tsaki, ta yadda duniya za ta kubuta daga mummunan tasirin sauyin yanayi, a kuma gudu tare a tsira tare.

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.