ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Sule Ya Gabatar da Kasafin ₦517.5bn Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Nasarawa

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Sule

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya miƙa kasafin kuɗin 2026 da ya kai darajar Naira biliyan 517.5 ga Majalisar Dokokin jihar, yana mai kiran shi “Kasafin Haɓaka Ci gaba”. A yayin gabatarwar da aka yi a Lafia, ya gode wa ’yan majalisar bisa yadda suke mara masa baya wajen tabbatar da ingantattun tsare-tsaren kuɗi. Ya ce kasafin ya yi daidai da manufar gwamnatinsa ta haɓaka masana’antu, karfafa manyan ayyuka da kuma ƙarfafa ci gaban tattalin arziki.

A cikin tsarin da ya gabatar, an ware N212.79bn (41.12%) don kashe-kashe na yau da kullum, yayin da N304.75bn za a karkatar zuwa manyan ayyukan raya kasa. Gwamnan ya ce irin wannan rabon ya nuna jajircewarsu wajen zuba jari a muhimman abubuwan more rayuwa da za su amfanar da jihar na dogon lokaci.

  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • Kotu Ta Sake Dakatar Da Sarki Ado Daga Gyara Fadar Nassarawa

Bangaren tattalin arziki ya samu mafi yawan kaso da N221.84bn, sannan bangaren zamantakewa ya karɓi N170.92bn, yayin da gine-gine suka samu N157.80bn. Haka kuma ilimi ya karɓi N92.91bn, tsaro da gudanarwa N142.96bn, tare da bangarori kamar lafiya, noma, muhalli da yawon bude ido da suka samu rabonsu.

ADVERTISEMENT

Da yake karɓar kundin kasafin, Kakakin Majalisar Dokoki, Dr. Danladi Jatau, ya tabbatar wa gwamna Sule cewa majalisar za ta yi aiki da sauri domin tabbatar da amincewa da kasafin. Ya jaddada bukatar ma’aikatu da hukumomi su kiyaye ka’idojin aiwatar da kasafi, ganin cewa bin tsari yana da tasiri wajen ingantacciyar gudanarwa. Ya kuma yaba da yadda gwamnati ke mayar da hankali kan ci gaban jama’a ta hanyar habaka fannonin da ke da tasiri kai tsaye a rayuwar al’umma.

Jatau ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da zaman lafiya da haɗin kai ba tare da la’akari da bambancin siyasa ko kabila ba. Ya ce nasarar kasafin kuɗi da aiwatar da shi yadda ya kamata na bukatar fahimta da goyon bayan jama’a. A cewarsa, aikin raya Nasarawa abu ne da ya wajaba a dauka da muhimmanci domin tabbatar da dorewar ci gaba a dukkan kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

Kakakin ya buƙaci al’umma su ci gaba da mara wa Gwamna Abdullahi Sule baya domin ganin an cimma burin da aka sa gaba na gina Nasarawa mai kwanciyar hankali da ci gaba. Ya ce majalisar za ta yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa kasafin 2026 ya zama wata kafa ta kara wa jihar kuzarin tattalin arziki da walwalar jama’a.

Sule
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness
  • Abubakar Sulaiman
    NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Next Post
Sheikh Zakzaky Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Sheikh Zakzaky Ya Miƙa Ta'aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.