• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Fitar Da Sakamakon Bincike Game Da Yadda Kanada Ke Nuna Wa Kayayyakinta Wariya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Fitar Da Sakamakon Bincike Game Da Yadda Kanada Ke Nuna Wa Kayayyakinta Wariya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Bayan da ta shafe tsawon rabin shekara tana gudanar da bincike da tattaro shaidu, a jiya Jumma’a kasar Sin ta fitar da sakamakon binciken da ta yi, game da yadda kasar Kanada take nuna wa kayayyakinta wariya, sakamakon da ya nuna cewa, irin matakin da Kanada ta dauka a shekarar da ta gabata, wato kara sanya harajin kwastam kan wasu hajojin da ta shigar daga kasar Sin, ciki har da motoci masu aiki da lantarki, da karafa da kuma sanholo, salo ne na nuna wariya. Don haka, kasar Sin ta mayar da martani bisa doka, inda ta kara sanya harajin kwastam kan wasu hajojin Kanada, al’amarin da ya sa aka fitar da rahoton bincike kan kin yarda da salon wariya, wanda ya zama irinsa na farko a duk fadin duniya.

A watan Agustan shekarar da ta gabata ne, kasar Kanada ta sanar da kara sanya harajin kwastam da kaso dari bisa dari, kan motoci masu aiki da karfin lantarki kirar kasar Sin, wanda ya fara aiki daga watan Oktoban shekara ta 2024, tare da kara harajin kwastam na kaso 25 bisa dari kan hajojin karafa da sanholo da kasar Sin ta samar. Makasudin yin hakan shi ne, hada baki da kasar Amurka, wajen sanyawa motoci masu aiki da karfin lantarki da kayan karafa da sanholo kirar kasar Sin harajin kwastam. Manazarta sun yi nuni da cewa, hajojin kasar Sin ne kadai, ita Kanada ta kara wa harajin kwastam, kuma ba tare da gudanar da cikakken bincike ba. Kana, fitar da irin wannan sanarwa ba tare da wata ingantacciyar hujja ba, salon wariya ne da Kanada ta yi, wanda ya kawo illa ga tsarin cinikayya na kasa da kasa.

  • A Mai Da Duniya Ta Zama Ta Kasa Da Kasa
  • Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Rahotannin sun kuma ruwaito cewa, a matsayinta na gani-kashe-nin Amurka, gwamnatin kasar Kanada ta sha nuna adawa da kasar Sin. Amma ba ta samu abun da take so ba. Tun bayan da sabuwar gwamnatin Amurka ta fara aiki tsawon kwanaki 40 ko fiye, ya zuwa yanzu, sau da dama ta ci zarafin Kanada, inda ta ce Kanada “jiha ce ta 51 a Amurka”, har ma ta yi mata barazana ta hanyar sanya harajin kwastam. Irin wannan abun ya zama gargadi ga wasu kasashe ’yan kalilan, wadanda ke fatan samun “afuwa” daga Amurka, bisa matakin da suka dauka kan kasar Sin.

Kasar Sin ba za ta rura wutar rikici ba, amma ba ta tsoro. Kuma tabbas za ta tsaya ga kiyaye muradun kasa da ikon samar da ci gaba, da kiyaye ka’idojin WTO game da tsarin cudanyar sassan kasa da kasa a fannin kasuwanci. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Kara Albarkatu Da Kudade Domin Tallafawa Samar Da Ayyukan Yi

Next Post

An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

Related

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

54 minutes ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

2 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

3 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

20 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

21 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

22 hours ago
Next Post
An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.