• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan barkewar annobar COVID-19, Amurka ta share fagen kirkiro karairayi, da labarai marasa maana, masu nuna yatsa ga kasar Sin, inda ta yi ta zargin Sin da laifin boye bayanai, ko kasancewa asalin bazuwar cutar. Irin wadannan labarai marasa tushe da yan siyasar Amurka suka rika bazawa, sun karkatar da tunanin Amurkawa, kuma burin yan siyasar shi ne kare gazawar su a fannin yaki da cutar a cikin gida yadda ya kamata.

Masharhanta da dama sun rika bayyana cewa, yan siyasar Amurka na kirkiro karin zarge-zarge, da siyasantar da batun wannan cuta, a matsayin wata dabara ta kawar da tunanin Amurkawa daga tarin matsalolin da ke addabar kasarsu, kama daga hauhawar farashi, da karyewar jarin bankuna, da koma bayan tattalin arziki da sauran su.

  • Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

A baya bayan nan, alkaluman kafofin watsa labarai na Amurka sun nuna cewa, Amurkawa da dama sun yarda cewa, annobar COVID-19 ta samo asali ne daga dakin gwajin kwayoyin cuta, sabanin bullar cutar daga yanayi na asali. Wadannan alkaluma dai sun yi daidai da raayin gwamnatin kasar, duk da cewa ba wasu shaidu na kimiyya da suka tabbatar da hakan.

Duk da cewa abu ne mai muhimmancin gaske a bi matakai da suka dace na gano asalin annobar COVID-19, domin yin kandagarkin aukuwar irin wannan annoba a gaba, ya dace a bi dabaru na kimiyya, da kwarewa domin tabbatar da hakan.

A watan Faburairun bara, hukumar kiwon lafiya ta MDD WHO, ta fitar da rahoton hadin gwiwa tare da kasar Sin game da asalin wannan cuta, bayan binciken makwanni 4 da aka gudanar a Sin, inda sakamakon ya tabbatar da cewa, zai yi matukar wuya, a ce wannan cuta ta bullo ne ta wani dakin gwajin kwayoyin cuta.

Labarai Masu Nasaba

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

A baya bayan nan, mun ga yadda Amurka ta sake dauko batun gano asalin wannan cuta, ta hanyar kaddamar da wani kudurin hukuma na gudanar da bincike, bisa dogaro da siyasa maimakon kimiyya. Ga alama dai yan siyasar Amurka suna son bin raayin kashin kai. Suna gamsuwa da kila-wa-kala, ko hasashe wajen tabbatar da zaton su, wanda hakan ya sabawa kwarewa, da shaidu da masana kimiyya ke amfani da su wajen tabbatar da asalin duk wata.

Illar wannan mataki shi ne karkatar da tunanin alumma daga gaskiya. Da amfani da siyasa a matsayin makamin cimma burin kashin kai, da haifar da rudani tsakanin alumma.

Gano asalin duk wata cuta na daukar lokaci mai yawa, kuma ya kamata yan siyasa su daina bata lokaci wajen furta kalamai marasa dalili, ko shaidun kimiyya. Kaza lika matakin yan siyasar Amurka na kin yin hadin gwiwa da masana kimiyya a wannan aiki, ba zai haifar da komai ba, illa kara muzanta kasarsu a idanun duniya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Next Post

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Related

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

12 hours ago
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

13 hours ago
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

14 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Manufar “Tsaunuka Biyu” Ta Sin Ta Samu Gagarumar Karbuwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Manufar “Tsaunuka Biyu” Ta Sin Ta Samu Gagarumar Karbuwa A Duniya

15 hours ago
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

16 hours ago
An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 
Daga Birnin Sin

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

17 hours ago
Next Post
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

August 15, 2025
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.