• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan barkewar annobar COVID-19, Amurka ta share fagen kirkiro karairayi, da labarai marasa maana, masu nuna yatsa ga kasar Sin, inda ta yi ta zargin Sin da laifin boye bayanai, ko kasancewa asalin bazuwar cutar. Irin wadannan labarai marasa tushe da yan siyasar Amurka suka rika bazawa, sun karkatar da tunanin Amurkawa, kuma burin yan siyasar shi ne kare gazawar su a fannin yaki da cutar a cikin gida yadda ya kamata.

Masharhanta da dama sun rika bayyana cewa, yan siyasar Amurka na kirkiro karin zarge-zarge, da siyasantar da batun wannan cuta, a matsayin wata dabara ta kawar da tunanin Amurkawa daga tarin matsalolin da ke addabar kasarsu, kama daga hauhawar farashi, da karyewar jarin bankuna, da koma bayan tattalin arziki da sauran su.

  • Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

A baya bayan nan, alkaluman kafofin watsa labarai na Amurka sun nuna cewa, Amurkawa da dama sun yarda cewa, annobar COVID-19 ta samo asali ne daga dakin gwajin kwayoyin cuta, sabanin bullar cutar daga yanayi na asali. Wadannan alkaluma dai sun yi daidai da raayin gwamnatin kasar, duk da cewa ba wasu shaidu na kimiyya da suka tabbatar da hakan.

Duk da cewa abu ne mai muhimmancin gaske a bi matakai da suka dace na gano asalin annobar COVID-19, domin yin kandagarkin aukuwar irin wannan annoba a gaba, ya dace a bi dabaru na kimiyya, da kwarewa domin tabbatar da hakan.

A watan Faburairun bara, hukumar kiwon lafiya ta MDD WHO, ta fitar da rahoton hadin gwiwa tare da kasar Sin game da asalin wannan cuta, bayan binciken makwanni 4 da aka gudanar a Sin, inda sakamakon ya tabbatar da cewa, zai yi matukar wuya, a ce wannan cuta ta bullo ne ta wani dakin gwajin kwayoyin cuta.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

A baya bayan nan, mun ga yadda Amurka ta sake dauko batun gano asalin wannan cuta, ta hanyar kaddamar da wani kudurin hukuma na gudanar da bincike, bisa dogaro da siyasa maimakon kimiyya. Ga alama dai yan siyasar Amurka suna son bin raayin kashin kai. Suna gamsuwa da kila-wa-kala, ko hasashe wajen tabbatar da zaton su, wanda hakan ya sabawa kwarewa, da shaidu da masana kimiyya ke amfani da su wajen tabbatar da asalin duk wata.

Illar wannan mataki shi ne karkatar da tunanin alumma daga gaskiya. Da amfani da siyasa a matsayin makamin cimma burin kashin kai, da haifar da rudani tsakanin alumma.

Gano asalin duk wata cuta na daukar lokaci mai yawa, kuma ya kamata yan siyasa su daina bata lokaci wajen furta kalamai marasa dalili, ko shaidun kimiyya. Kaza lika matakin yan siyasar Amurka na kin yin hadin gwiwa da masana kimiyya a wannan aiki, ba zai haifar da komai ba, illa kara muzanta kasarsu a idanun duniya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Next Post

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

10 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

12 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

12 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

14 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

14 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

16 hours ago
Next Post
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.