ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

by CMG Hausa
3 years ago
Covid-19

Tun bayan barkewar annobar COVID-19, Amurka ta share fagen kirkiro karairayi, da labarai marasa maana, masu nuna yatsa ga kasar Sin, inda ta yi ta zargin Sin da laifin boye bayanai, ko kasancewa asalin bazuwar cutar. Irin wadannan labarai marasa tushe da yan siyasar Amurka suka rika bazawa, sun karkatar da tunanin Amurkawa, kuma burin yan siyasar shi ne kare gazawar su a fannin yaki da cutar a cikin gida yadda ya kamata.

Masharhanta da dama sun rika bayyana cewa, yan siyasar Amurka na kirkiro karin zarge-zarge, da siyasantar da batun wannan cuta, a matsayin wata dabara ta kawar da tunanin Amurkawa daga tarin matsalolin da ke addabar kasarsu, kama daga hauhawar farashi, da karyewar jarin bankuna, da koma bayan tattalin arziki da sauran su.

  • Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

A baya bayan nan, alkaluman kafofin watsa labarai na Amurka sun nuna cewa, Amurkawa da dama sun yarda cewa, annobar COVID-19 ta samo asali ne daga dakin gwajin kwayoyin cuta, sabanin bullar cutar daga yanayi na asali. Wadannan alkaluma dai sun yi daidai da raayin gwamnatin kasar, duk da cewa ba wasu shaidu na kimiyya da suka tabbatar da hakan.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa abu ne mai muhimmancin gaske a bi matakai da suka dace na gano asalin annobar COVID-19, domin yin kandagarkin aukuwar irin wannan annoba a gaba, ya dace a bi dabaru na kimiyya, da kwarewa domin tabbatar da hakan.

A watan Faburairun bara, hukumar kiwon lafiya ta MDD WHO, ta fitar da rahoton hadin gwiwa tare da kasar Sin game da asalin wannan cuta, bayan binciken makwanni 4 da aka gudanar a Sin, inda sakamakon ya tabbatar da cewa, zai yi matukar wuya, a ce wannan cuta ta bullo ne ta wani dakin gwajin kwayoyin cuta.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

A baya bayan nan, mun ga yadda Amurka ta sake dauko batun gano asalin wannan cuta, ta hanyar kaddamar da wani kudurin hukuma na gudanar da bincike, bisa dogaro da siyasa maimakon kimiyya. Ga alama dai yan siyasar Amurka suna son bin raayin kashin kai. Suna gamsuwa da kila-wa-kala, ko hasashe wajen tabbatar da zaton su, wanda hakan ya sabawa kwarewa, da shaidu da masana kimiyya ke amfani da su wajen tabbatar da asalin duk wata.

Illar wannan mataki shi ne karkatar da tunanin alumma daga gaskiya. Da amfani da siyasa a matsayin makamin cimma burin kashin kai, da haifar da rudani tsakanin alumma.

Gano asalin duk wata cuta na daukar lokaci mai yawa, kuma ya kamata yan siyasa su daina bata lokaci wajen furta kalamai marasa dalili, ko shaidun kimiyya. Kaza lika matakin yan siyasar Amurka na kin yin hadin gwiwa da masana kimiyya a wannan aiki, ba zai haifar da komai ba, illa kara muzanta kasarsu a idanun duniya.

 

Covid-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Next Post
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.