Rundunar Sojojin Nijeriya Operation Safe Haven sun kama wani mutum da ake zargin ɗan fashi ne a Zangon Kataf ta jihar Kaduna.
A cewar wata sanarwa daga mai magana da yawun Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, an kama mutumin ne yana sanye da kayan Soja domin ya yi kama da Soja wajen kai hare-hare. An ƙwato daga gare shi bindigar AK-47, harsasai 3, katin shaidar ɗan vijilante, da wayar hannu da katunan cirar kuɗin 2.
- Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya
- Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
A wani lamari daban kuma, Sojojin sun dirkewo wani gidan ‘yan bindiga a Kwanar Lauje, ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Filato. Ko da yake ‘yan ƙungiyar sun gudu kafin Sojojin su isa, an samu tarin makamai ciki har da bindigar AK-47, da harsasai 300, da harsasai na bindigar kakkaɓo jirgi (anti-aircraft).
Manjo Zhakom ya bayyana cewa an ajiye duk waɗannan kayayyakin yayin da Sojojin ke ci gaba da bincike don kama ‘yan kungiyar da suka tsere.
Ya kuma tabbatar da cewa Sojojin za su ci gaba da kai farmaki kan masu laifi a yankin domin tabbatar da zaman lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp