ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Fara Binciken Kuskuren Kashe Fararen Hula Da ‘Yan Sa-kai A Zamfara

by Sadiq
2 years ago
Sojoji

Rundunar Sojin Saman Nijeriya, ta bayyana cewa tana gudanar da bincike kan rahotannin da ke cewa fararen hula 16, ciki har da ‘yan sa-kai, sun rasa rayukansu a harin sama da aka kai a ƙauyen Tungar Kara da ke Jihar Zamfara.

Rahotannin sun nuna cewa harin, wanda aka kai don fatattakar ‘yan bindiga, ya afka wa wasu ‘yan sa-kai na Jihar Zamfara da fararen hula waɗanda suka haɗu domin kare kansu daga hare-haren ‘yan bindiga.

  • Huldar Sin Da Afirka Za Ta Zama Abin Koyi Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ta Daukacin Bil’adama
  • Gwamnatin Kano Ta Raba Kayan Makaranta Kyauta Ga Dalibai 789,000

Mai magana da yawun rundunar, Olusola F. Akinboyewa, ya ce sojin sama na ɗaukar rayukan ‘yan Nijeriya da muhimmanci.

ADVERTISEMENT

Ya kuma tabbatar da cewa za a yi cikakken bincike kan lamarin domin gano gaskiyar abin da ya faru da kuma sanar da jama’a sakamakon binciken.

A nata ɓangaren, gwamnatin Jihar Zamfara ta nuna alhininta ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa.

LABARAI MASU NASABA

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa harin ya afka wa ‘yan sa-kai da aka ɗauka ‘yan bindiga ne, yayin da suke ƙoƙarin kare jama’a daga hare-haren ‘yan bindiga.

Kurakuran Irin Waɗannan Hare-hare A Baya

Irin wannan kuskuren ba sabon abu ba ne a yaƙin da ake yi da ta’addanci a Nijeriya.

A shekarar 2023, wani harin sama ya afka wa taron Maulidi a Tudun Biri, da ke Jihar Kaduna, inda aka rasa rayukan mutum 85.

Haka kuma, a 2017, harin sama ya kashe mutum 112 a sansanin ‘yan gudun hijira a Rann kusa da iyakar Nijeriya da Kamaru.

Waɗannan lamura sun ƙara nuna ƙalubalen da hukumomin tsaro ke fuskanta wajen tantance mayaƙa da fararen hula, lamarin da ke haifar da mummunan asarar rayuka.

Wannan yana buƙatar sake nazari kan yadda ake gudanar da hare-haren sama don rage irin wannan iftila’i.

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Ɓangaren Bafarawa Kan Rikicin Shugabannin PDP A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.