• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Sojoji

Hadakar jami’an tsaro sojin kasa da na ruwa sun hallaka ‘yan bindiga bakwai a yayin wani samamen kakkebe ‘yan ta’adda a yankin Kasso da ke karamar hukumar Chikum a Jihar Kaduna.

A wata sanarwar manema labarai da Kwamishinan Kula da Harkokin Tsaron Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, bayanan da gwamnatin Jihar Kaduna ta samu na sakamakon aikin, ya yi nuni da cewa sojojin sun cimma ‘yan bindigae ne a wajen kauyen Ungwani Rimi da ke Kasso a kusa da wani ruwa.

  • NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a
  • Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba –Matasan Arewa A Kudu

Sanarwar ta ce, haduwar tasu ke da wuya sojojin sun sha karfin ‘yan bindigar a lokacin da suka gwabza fada a tsakaninsu.

Aruwan, ya kara da cewa sojojin sun kwato babura guda biyar, alburusai guda 153, da wasu alburusai guda bakwai tare da wayoyin hannu guda uku a lokacin arangamar.

“’Yan bindiga bakwai ne aka tabbatar da kashesu a yayin harin, tare da tunanin wasu ma za su iya bin sawunsu da wadanda suka jikkata a kusa da wani kogi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

“Lokacin da ya samu rahoton, gwamna Nasiru El-Rufai ya jinjina tare da yaba wa kokarin dakarun sojojin tare da fatan za su kara ninka kokarinsu domin dakile aniyar ‘yan bindiga a jihar

“Sannan, gwamnan ya kuma jinjina wa jagorancin Manjo-Janar TA Lagbaja, GOC na runduna ta daya da Cdre ME Ejumabone, kwamandan kwalejin horas da sojojin ruwa NNSAT, bisa nasarorin da suka samu,” in ji Aruwan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Next Post
Tsarin Zamanantar Da Kasar Sin Wani Tsari Ne Na Inganta Da Kare Hakkin Dan Adam Daki-daki

Tsarin Zamanantar Da Kasar Sin Wani Tsari Ne Na Inganta Da Kare Hakkin Dan Adam Daki-daki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.