• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Kaduna

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Sojojin Sama

Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (NAF) ta sanar da cewa ɓangaren Sojojin sama na Operation Whirl Stroke sun kai hare-hare ta sama wanda ya hallaka ‘yan ta’adda da dama a maɓoyarsu da ke ƙananan Hukumomin Giwa da Igabi na Jihar Kaduna.

A cewar wata sanarwa da AVM Edward Gabkwet, Daraktan hulɗa da Jama’a ya fitar, ana ci gaba da samun nasara a waɗannan hare-haren duk da matsalolin yanayi da ke addabar yankin Arewa maso Yamma.

  • Mutane 20 Sun Mutu, 52 Sun Ji Rauni A Harin Bam A Borno – DHQ
  • Sabbin Hare-haren Kunar Bakin Wake A Borno Jama’a Na Fargabar Jiya Ta Dawo Yau

Ɗaya daga cikin hare-haren da aka kai shi ne a ranar Juma’a a maɓoyar Alhaji Layi dake ƙauyen Kufan Shantu, ƙaramar hukumar Giwa, inda aka lalata kayan aiki da ‘yan ta’addan suka ɓoya a ƙarƙashin bishiyoyi.

An samu nasarar kai wani hari a ranar Asabar a sansanin ‘yan ta’adda a cikin dajin Malum da ke ƙaramar hukumar Igabi. Harin dai an kai shi ne bayan samun cikakkun kwararan bayanan sirri, tare da gudanar da lissafi da leken asiri, ya kashe mafi yawan ‘yan ta’addan da aka gani suna yawo a cikin dajin.

Waɗannan hare-haren ta sama an yi su ne sakamakon bayanan sirri da suka nuna wuraren da aka nufa a matsayin maboyar ‘yan ta’addan da suka kai hari kan sojoji a Manini a ranar 10 ga Yuli.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

AVM Gabkwet ya jaddada cewa NAF, tare da haɗin gwuiwar Sojojin ƙasa, za su ci gaba da samun rinjaye ta hanyar lura da yanayi, da gudanar da sintiri akai-akai, da kuma kai hare-hare kai tsaye kan maɓoyar ‘yan ta’adda. Wannan dabarar na nufin kawar da ta’addanci da sauran laifuka a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Sufeta Janar Na Ƙasa Ya Dakatar Da Aiwatar Da Na’urar E-CMR Bayan Shan Suka

Sufeta Janar Na Ƙasa Ya Dakatar Da Aiwatar Da Na'urar E-CMR Bayan Shan Suka

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.