ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Ƙwayar Tiramadol 396,000 A Filin Jirgin Saman Yola

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
NDLEA

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) sun kama kwantena 396,000 na Kwayar tramadol a Filin Jirgin Sama na Aliyu Mustapha, Yola.

Wannan sabon kamen ya zo ne kasa da sati guda bayan hukumar ta samu fiye da kwantena 171,000 ta tramadol a lokacin wasu ayyukan daban a jihohin Neja, Binuwe, da Taraba.

  • Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho
  • Gwamnan Neja Ya Yi Allah-Wadai Da Sace Ɗaliban St. Mary A Papiri

A cikin sanarwa da aka fitar, kakakin NDLEA, Femi Babafemi, ya bayyana cewa wani mutum mai shekaru 50, Ahmed Nda, an kama shi akan wannan laifi.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, “A Jihar Adamawa, jami’an NDLEA sun samu kwantena 396,000 ta kwayar tramadol daga hannun wani mutum, Ahmed Isyaku Nda, mai shekaru 50, a Filin Jirgin Sama na Aliyu Mustapha, Yola, yayin da aka samu kilo 785 na skunk a cikin ma’ajiyar wani mai sayar da kwayoyi da ke gudun hijira a Asob Maraba Karu, Jihar Nasarawa.”

A wani labari mai alaka, Babafemi ya tabbatar da kama wani babban mai safarar kwayoyi da ake nema wanda ya yi basaja a matsayin mai aiki a karkashin kasuwanci da Otal.

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

“Wannan mutum mai shekaru 42, Ibemesi, wanda shi ne MD/CEO na Franc CJ Ibemesi Nig. Ltd, an kama shi a otal dinsa na Daisy Garden Hotel, 66–68 Agbeke Street, Ago Palace Way, Isolo, Lagos, da sassafe.”

“Daga bisani an kai shi zuwa ma’ajiyarsa a 7 Pius Ezeobi Street, Off Ago Palace Way, Isolo, inda aka samu jakunkuna 42 manya da kwalaye hudu na Loud, wani nau’in tabar wiwi, da nauyin kilo 1,762.8.

“Haka kuma, an kwato Dala 11,600, da Fam 2,000 na Birtaniya, da Euro 2,200, da Dalar Kanada 50, duka a cikin kudi na hannu,” in ji Babafemi.

Har ila yau, ya bayyana cewa an tarwatsa yunkurin wata kungiyar safarar kwayoyi da ke aiki daga dajin Orita-Apeje, Araromi-Okeodo a Karamar Hukumar Ife ta Kudu, Jihar Osun, na rarraba kilo 11,135 na skunk da aka sarrafa, bayan kwanaki na leken asiri.

A cewarsa, “An kwato motoci biyu da ake amfani da su wajen safarar kayan haramtacciyar — mota Bolbo mai lambar WWR 29 DA da mota Mercedes mai lambar rajista AWK 713 YZ — sannan an kama mutum bakwai.”

Mutanen da ke hannun hukumar, a cewar Babafemi, sun hada da Lucky Abiodun, Julius Amos, Bictor Ngbikili, Sunday Oduegwu, Ibrahim Akanni, Eze Godstime, da Fred Ifeanyichukwu.

Yayin yabawa da jami’an da suka shiga cikin ayyukan daban-daban, Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya yi kira ga duk ma’aikatan a fadin kasar da su ci gaba da bin tsarin kula da kwayoyi na hukumar daidai da hadin kai.

Wani rahoto daga PUNCH Metro ranar Talata ya bayyana wani sabon aikin leken asiri inda NDLEA ta kwato haramtattun kayan da ke da darajar kimanin Naira biliyan 338 a tashar PTML ta Tin Can Island Port a Legas.

Hukumar ta ce tana yin hadin gwiwa da US DEA da National Crime Agency ta Birtaniya domin gano wadanda ke da alhakin wannan kaya.

A wani labari mai alaka da wannan, Babafemi ya tabbatar da kama wani babban mai safarar kwayoyi da ake nema wanda ya yi basaja a matsayin dan kasuwa da ke zaune a wani Otal

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
NDLEA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • Sulaiman
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • Sulaiman
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

MASU ALAKA

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi
Tsaro

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Next Post
Firaministan Sin Ya Ce A Shirye Yake Ya Yi Aiki Da Zambiya Da Tanzaniya Wajen Gina Sabuwar Cibiyar Tattalin Arziki

Firaministan Sin Ya Ce A Shirye Yake Ya Yi Aiki Da Zambiya Da Tanzaniya Wajen Gina Sabuwar Cibiyar Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.