• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sudan: Jami’o’in Nijeriya Sun Sha Alwashin Bai Wa Daliban Da Aka Kwaso Guraben Karatu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Sudan

Wasu Jami’o’i Nijeriya sun sha alwashin taimaka wa daliban da aka kwasho daga kasar Sudan sakamakon yakin da ke ci gaba da kamari a kasar.

A wata sanarwar da hukumar kula da ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM) ta fitar a ranar Asabar, ta ce, Jami’o’i da dama ne suka nuna sha’awarsu na daukan daliban Nijeriya da aka dawo da su daga Sudan da suka hada da jami’ar Igbinedion, Okada, da ke jihar Edo, jami’ar Summit, Offa, jihar Kwara, da jami’ar American University, the Gambia da dai sauransu.

  • Wane Ya Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa?
  • Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

LEADERSHIP ta labarto cewa, hukumar samar da guraben karatu ta kasa (JAMB) ta yi alkawarin samar da dukkanin taimakon da suka dace wajen tabbatar da daliban Nijeriya da aka kwaso daga Sudan sun samu shiga cikin Jami’o’in da suke kasar domin cigaba da karatunsu.

Shugabar hukumar NIDCOM Hon. Abike Dabiri-Erewa, ta yaba da kokarin da azamar jami’ar Igbinedion sa’ilin da ta amshi bakwancin mukaddashin shugaban jami’ar Farfesa Lawrence Ikechukwu Ezemonye a Abuja.

Abike ta nuna bukatar da ke akwai na cewa kowa ya bi ka’idar da JAMB ta gindaya domin kauce wa kowace irin matsala da ka iya biyo baya.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

“Mun kasance tare da JAMB kuma JAMB din ta bayar da sharadi da ka’idojin da za a yi, na tabbatar kana sane don haka idan sun zo maka kana iya shigar da su, za mu bukaci wasika daga JAMB D’s ke tabbatar da cewa JAMB din ta bayar da izirin karatu, yin hakan zai sa a samu kauce wa matsalar fs mutum idan ya kammala karatu kada a zo a ce ba zai je hidimta wa kasa ba,” ta shaida.

Ta kuma shaida cewar zuwa yanzu ‘yan Nijeriya 2,371 ne aka kwaso daga Suzan zuwa Nan gida Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
An Jefar Da Jariri Dan Kwana 2 A Sansanin ‘Yan Gundun Hijira A Edo

An Jefar Da Jariri Dan Kwana 2 A Sansanin 'Yan Gundun Hijira A Edo

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.