ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Bagudu

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na Jihar Kebbi, ya gabatar da takardun shaida a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Birnin Kebbi, inda ya ke kalubalantar nasarar lashe zaben Sanata Muhammadu Adamu Aliero, PDP da INEC a gaban kotun ta hanyar lauyansa.

Idan za a tuna dai Bagudu yana kalubalantar nasarar da Sanata Aliero ya samu kan zaben Sanatan Kebbi ta tsakiya da ya gudana a kwanakin baya.

  • Nijeriya Za Ta Yi Kawance Da WHO Kan Rigakafi
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

Ci gaba da gabatar da takardun wani bangare ne na zaman sauraren karar na matakin farko na sauraren karar da ya shigar da kuma neman kotu ta karbe su a matsayar shaida kamar yadda dokar zabe ta tanada.

ADVERTISEMENT

Lauyan Gwamna Bagudu, Barista Lagalo D. Lagalo, ya ce, “A karamar hukumar Kalgo mun nemi gabatar da fom 32 na EC8A1, amma 30 ne kawai a wurinsu biyu ba su samu ba, sun gabatar da fom guda 8 na EC 8C1. Ya kuma mika fom din EC8C1 na kananan hukumomi guda takwas wadanda su ne suka hada gundumar Kebbi ta tsakiya ta jihar a matsayin wani bangare na takardun shakda ga abin da yake kalubalantar ga zaben na Sanata Muhammadu Adamu Aliero.”

Haka kuma ya gabatar da fom daya na takardar takaitaccen sakamako na EC8B1 watau (summary results sheet) da kuma nau’i daya na EC8E1 bayyana sakamakon zabe. Daga nan sai ya sanar da kotun cewa, “Duk takardun da aka jera a shafi na 28,29, 30,31 da 34 ba su samuwa, amma za a gabatar da su a ranar da za a dawo zaman na gaba,” in ji shi”.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

“Duk da haka, har yanzu a karamar hukumar Kalgo mun lissafta fom biyu EC40G (pu) amma daya ne kawai ake samu a mazaba ta uku a runfa ta daya. Ya bayyana wa kotun cewa a zaman na yau abin da suke da shi ke nan. Amma a ranar da aka sanya don dawowa zaman Kotun na gaba za a gabatar da duk takardun da aka bayyana cewa babusu a hannu za a tabbatar da cewa an gabatar da su a gaban kotun.”

Kazalika, Barista Lagalo ya tabbatar wa kotun za a shigar da takardun a ranar da za a dawo zaman Kotun daga bisani kuma ya nemi a dage zaman har zuwa ranar Litinin 15 ga watan Mayu na shekara ta 2023 don kammala gabatar da shedar takardu.

A bangarensu Lauyan sanata Adamu Aliero, Barrister Aminu Hassan a matsayin wadanda ake kara na farko, lauyan PDP a matsayar wadanda ake kara na biyu D.D Dodo SAN wanda lauyan hukumar INEC da ake kara na uku Barrister Magnus Ihejirika ya tsayawa yayin gabatar da shaidar takardun a gabn kotun sun amince da dage cigaba da Shari’ar zuwa ranar Litinin 15 ga watan da muke ciki.

Kotun ta amince da takaddun da aka gabatar a gabanta kuma an yi musu alama azaman Nunin AAB1 zuwa AAB 16, AAB17G, AAB 19 da AAB 20 bi da bi.

Shugabar kotun, Honourable Justice Margret Opara ta ce, “Bisa yarjejeniyar da lauyoyin na dukkan bangarori suka amince an dage sauraren karar zuwa ranar Litinin 15 ga Mayu 2023 don ci gaba da zaman sauraron karar.

Bagudu
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.