• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na Jihar Kebbi, ya gabatar da takardun shaida a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Birnin Kebbi, inda ya ke kalubalantar nasarar lashe zaben Sanata Muhammadu Adamu Aliero, PDP da INEC a gaban kotun ta hanyar lauyansa.

Idan za a tuna dai Bagudu yana kalubalantar nasarar da Sanata Aliero ya samu kan zaben Sanatan Kebbi ta tsakiya da ya gudana a kwanakin baya.

  • Nijeriya Za Ta Yi Kawance Da WHO Kan Rigakafi
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

Ci gaba da gabatar da takardun wani bangare ne na zaman sauraren karar na matakin farko na sauraren karar da ya shigar da kuma neman kotu ta karbe su a matsayar shaida kamar yadda dokar zabe ta tanada.

Lauyan Gwamna Bagudu, Barista Lagalo D. Lagalo, ya ce, “A karamar hukumar Kalgo mun nemi gabatar da fom 32 na EC8A1, amma 30 ne kawai a wurinsu biyu ba su samu ba, sun gabatar da fom guda 8 na EC 8C1. Ya kuma mika fom din EC8C1 na kananan hukumomi guda takwas wadanda su ne suka hada gundumar Kebbi ta tsakiya ta jihar a matsayin wani bangare na takardun shakda ga abin da yake kalubalantar ga zaben na Sanata Muhammadu Adamu Aliero.”

Haka kuma ya gabatar da fom daya na takardar takaitaccen sakamako na EC8B1 watau (summary results sheet) da kuma nau’i daya na EC8E1 bayyana sakamakon zabe. Daga nan sai ya sanar da kotun cewa, “Duk takardun da aka jera a shafi na 28,29, 30,31 da 34 ba su samuwa, amma za a gabatar da su a ranar da za a dawo zaman na gaba,” in ji shi”.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

“Duk da haka, har yanzu a karamar hukumar Kalgo mun lissafta fom biyu EC40G (pu) amma daya ne kawai ake samu a mazaba ta uku a runfa ta daya. Ya bayyana wa kotun cewa a zaman na yau abin da suke da shi ke nan. Amma a ranar da aka sanya don dawowa zaman Kotun na gaba za a gabatar da duk takardun da aka bayyana cewa babusu a hannu za a tabbatar da cewa an gabatar da su a gaban kotun.”

Kazalika, Barista Lagalo ya tabbatar wa kotun za a shigar da takardun a ranar da za a dawo zaman Kotun daga bisani kuma ya nemi a dage zaman har zuwa ranar Litinin 15 ga watan Mayu na shekara ta 2023 don kammala gabatar da shedar takardu.

A bangarensu Lauyan sanata Adamu Aliero, Barrister Aminu Hassan a matsayin wadanda ake kara na farko, lauyan PDP a matsayar wadanda ake kara na biyu D.D Dodo SAN wanda lauyan hukumar INEC da ake kara na uku Barrister Magnus Ihejirika ya tsayawa yayin gabatar da shaidar takardun a gabn kotun sun amince da dage cigaba da Shari’ar zuwa ranar Litinin 15 ga watan da muke ciki.

Kotun ta amince da takaddun da aka gabatar a gabanta kuma an yi musu alama azaman Nunin AAB1 zuwa AAB 16, AAB17G, AAB 19 da AAB 20 bi da bi.

Shugabar kotun, Honourable Justice Margret Opara ta ce, “Bisa yarjejeniyar da lauyoyin na dukkan bangarori suka amince an dage sauraren karar zuwa ranar Litinin 15 ga Mayu 2023 don ci gaba da zaman sauraron karar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BaguduKaraKebbiKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayani A Kan Starlink, Da Yadda Tsarinsa Yake

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

2 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

3 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

3 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

5 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

5 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

7 hours ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.