ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Bagudu

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na Jihar Kebbi, ya gabatar da takardun shaida a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Birnin Kebbi, inda ya ke kalubalantar nasarar lashe zaben Sanata Muhammadu Adamu Aliero, PDP da INEC a gaban kotun ta hanyar lauyansa.

Idan za a tuna dai Bagudu yana kalubalantar nasarar da Sanata Aliero ya samu kan zaben Sanatan Kebbi ta tsakiya da ya gudana a kwanakin baya.

  • Nijeriya Za Ta Yi Kawance Da WHO Kan Rigakafi
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

Ci gaba da gabatar da takardun wani bangare ne na zaman sauraren karar na matakin farko na sauraren karar da ya shigar da kuma neman kotu ta karbe su a matsayar shaida kamar yadda dokar zabe ta tanada.

ADVERTISEMENT

Lauyan Gwamna Bagudu, Barista Lagalo D. Lagalo, ya ce, “A karamar hukumar Kalgo mun nemi gabatar da fom 32 na EC8A1, amma 30 ne kawai a wurinsu biyu ba su samu ba, sun gabatar da fom guda 8 na EC 8C1. Ya kuma mika fom din EC8C1 na kananan hukumomi guda takwas wadanda su ne suka hada gundumar Kebbi ta tsakiya ta jihar a matsayin wani bangare na takardun shakda ga abin da yake kalubalantar ga zaben na Sanata Muhammadu Adamu Aliero.”

Haka kuma ya gabatar da fom daya na takardar takaitaccen sakamako na EC8B1 watau (summary results sheet) da kuma nau’i daya na EC8E1 bayyana sakamakon zabe. Daga nan sai ya sanar da kotun cewa, “Duk takardun da aka jera a shafi na 28,29, 30,31 da 34 ba su samuwa, amma za a gabatar da su a ranar da za a dawo zaman na gaba,” in ji shi”.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Duk da haka, har yanzu a karamar hukumar Kalgo mun lissafta fom biyu EC40G (pu) amma daya ne kawai ake samu a mazaba ta uku a runfa ta daya. Ya bayyana wa kotun cewa a zaman na yau abin da suke da shi ke nan. Amma a ranar da aka sanya don dawowa zaman Kotun na gaba za a gabatar da duk takardun da aka bayyana cewa babusu a hannu za a tabbatar da cewa an gabatar da su a gaban kotun.”

Kazalika, Barista Lagalo ya tabbatar wa kotun za a shigar da takardun a ranar da za a dawo zaman Kotun daga bisani kuma ya nemi a dage zaman har zuwa ranar Litinin 15 ga watan Mayu na shekara ta 2023 don kammala gabatar da shedar takardu.

A bangarensu Lauyan sanata Adamu Aliero, Barrister Aminu Hassan a matsayin wadanda ake kara na farko, lauyan PDP a matsayar wadanda ake kara na biyu D.D Dodo SAN wanda lauyan hukumar INEC da ake kara na uku Barrister Magnus Ihejirika ya tsayawa yayin gabatar da shaidar takardun a gabn kotun sun amince da dage cigaba da Shari’ar zuwa ranar Litinin 15 ga watan da muke ciki.

Kotun ta amince da takaddun da aka gabatar a gabanta kuma an yi musu alama azaman Nunin AAB1 zuwa AAB 16, AAB17G, AAB 19 da AAB 20 bi da bi.

Shugabar kotun, Honourable Justice Margret Opara ta ce, “Bisa yarjejeniyar da lauyoyin na dukkan bangarori suka amince an dage sauraren karar zuwa ranar Litinin 15 ga Mayu 2023 don ci gaba da zaman sauraron karar.

Bagudu
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.