ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jefar Da Jariri Dan Kwana 2 A Sansanin ‘Yan Gundun Hijira A Edo

An Tsinci Jaririn Dauke Da Rubutaccen Sako

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Jariri

An tsinci jariri da ake zargin dan kwana biyu ne a duniya da aka yasar a harabar sansanin ‘yan gundun hijira a yankin Uhogia kusa da Benin, da ke Ovia a Jihar Edo.

Kodinetan da ke kula da sansanin, Fasto Solomon Folorunsho, ne ya sanar da hakan lokacin da ke gana wa da ‘yan jarida a ranar Juma’a, ya ce, jaririn ya na tsananin bukatar nonon shayarwa.

  • Sudan: Jami’o’in Nijeriya Sun Sha Alwashin Bai Wa Daliban Da Aka Kwaso Guraben Karatu
  • Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

A cewarsa, wata da ba san ko wace ce ba ta yasar da jaririn a kofar shiga sansanin tare da rubutaccen sako a jikinsa a ranar Juma’a da misalin karfe 11 na safiya.

ADVERTISEMENT

Ya ce yanzu haka jaririn na kan kulawar Likitoci a asibitin sansanin, “Mun gano jaririn dan kwanaki biyu ne da aka yasar a mashigar Sansanin dauke da sako a rubuce.

“Jaririn da aka yasar tare da rubutaccce sako da ke cewa ‘don Allah ku taimakeni ku kula da shi. Ba zan iya kulawa da shi ba ne, saboda bana da komai da zan iya ciyar da shi, kuma tabbas bana son kasheshi, don haka yanzu ya zama mallakinku don Allah’.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Kodinetan ya ce sun sanar da ‘yansanda, ma’aikatar kula da harkokin mata da DSS kan wannan lamarin.

Kazalika, Folorunsho ya roki mahaifiyar jaririn da ta fito don Allah ta bayyana kanta domin jaririn na tsananin bukatar shayarwa.

“Ina karfafar mahaifiyarsa da ta zo kada ta ji wani tsaro ta fito ta bayyana kanta domin yaron ya samu nonon uwa, in kuma hakan bai samu ba za mu nemi Madara a ke bayarwa yaro, don haka za mu nema musu tallafi.

“Ko kuma za mu san yadda za mu yi mu tara kudi mu kama wa mahaifiyarsa din gidan haya, mu taimaka da abincin da sauran kayan bukata, tun da ta ce dalilin yasar da jaririn kawai don ba za ta iya daukan nauyin yaron ba ne. To ta fito za a taimaka mata sosai.

“Na tabbatar idan da wannan tallafin mahaifiyarsa za ta kula da jaririn.”

“Amma idan mun yi duk mai yiyuwa hakan bai samu ba, za mu cigaba da kula da jaririn.”

Folorunsho, ya roki ‘yan Nijeriya da su taimaka wa jaririn da kayan sawa kayan abinci da sauran kayan da jariri ke bukata.

Jariri
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Hukumar Abinci Ta Duniya Ta Ce A Karon Farko Farashin Abinci Ya Tashi

Hukumar Abinci Ta Duniya Ta Ce A Karon Farko Farashin Abinci Ya Tashi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.