ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jefar Da Jariri Dan Kwana 2 A Sansanin ‘Yan Gundun Hijira A Edo

An Tsinci Jaririn Dauke Da Rubutaccen Sako

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Jariri

An tsinci jariri da ake zargin dan kwana biyu ne a duniya da aka yasar a harabar sansanin ‘yan gundun hijira a yankin Uhogia kusa da Benin, da ke Ovia a Jihar Edo.

Kodinetan da ke kula da sansanin, Fasto Solomon Folorunsho, ne ya sanar da hakan lokacin da ke gana wa da ‘yan jarida a ranar Juma’a, ya ce, jaririn ya na tsananin bukatar nonon shayarwa.

  • Sudan: Jami’o’in Nijeriya Sun Sha Alwashin Bai Wa Daliban Da Aka Kwaso Guraben Karatu
  • Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

A cewarsa, wata da ba san ko wace ce ba ta yasar da jaririn a kofar shiga sansanin tare da rubutaccen sako a jikinsa a ranar Juma’a da misalin karfe 11 na safiya.

ADVERTISEMENT

Ya ce yanzu haka jaririn na kan kulawar Likitoci a asibitin sansanin, “Mun gano jaririn dan kwanaki biyu ne da aka yasar a mashigar Sansanin dauke da sako a rubuce.

“Jaririn da aka yasar tare da rubutaccce sako da ke cewa ‘don Allah ku taimakeni ku kula da shi. Ba zan iya kulawa da shi ba ne, saboda bana da komai da zan iya ciyar da shi, kuma tabbas bana son kasheshi, don haka yanzu ya zama mallakinku don Allah’.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Kodinetan ya ce sun sanar da ‘yansanda, ma’aikatar kula da harkokin mata da DSS kan wannan lamarin.

Kazalika, Folorunsho ya roki mahaifiyar jaririn da ta fito don Allah ta bayyana kanta domin jaririn na tsananin bukatar shayarwa.

“Ina karfafar mahaifiyarsa da ta zo kada ta ji wani tsaro ta fito ta bayyana kanta domin yaron ya samu nonon uwa, in kuma hakan bai samu ba za mu nemi Madara a ke bayarwa yaro, don haka za mu nema musu tallafi.

“Ko kuma za mu san yadda za mu yi mu tara kudi mu kama wa mahaifiyarsa din gidan haya, mu taimaka da abincin da sauran kayan bukata, tun da ta ce dalilin yasar da jaririn kawai don ba za ta iya daukan nauyin yaron ba ne. To ta fito za a taimaka mata sosai.

“Na tabbatar idan da wannan tallafin mahaifiyarsa za ta kula da jaririn.”

“Amma idan mun yi duk mai yiyuwa hakan bai samu ba, za mu cigaba da kula da jaririn.”

Folorunsho, ya roki ‘yan Nijeriya da su taimaka wa jaririn da kayan sawa kayan abinci da sauran kayan da jariri ke bukata.

Jariri
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Hukumar Abinci Ta Duniya Ta Ce A Karon Farko Farashin Abinci Ya Tashi

Hukumar Abinci Ta Duniya Ta Ce A Karon Farko Farashin Abinci Ya Tashi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.