Wasu mazauna yankin sun kashe daya daga cikin ‘yan fashin da ke dauke da wasu gungun ‘yan fashi da makami biyar da suka kai hari Abule-Ijoko a Karamar Hukumar Ifo da ke jihar Ogun.
Majiyarmu ta samu labarin cewa ‘yan fashin dauke da bindiga kirar gida da kuma adda, sun afka wasu gidaje biyu da wasu matasa suka mamaye a daren a wannan ranar suka kwace musu wayoyi da kwamfutar tafi-da-gidanka.
A cewar rahoton, daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su ya yi karfin gwiwa sannan ya tunkari ‘yan fashin a lokacin sun kwashe masa tufafinsa bayan sun tattara wayarsa. Ko da yake rahotanni sun ce ’yan fashin sun arce daga wurin da ganimar amma daya daga cikinsu bai yi sa’a ba kasancewar an rike shi kuma an yi masa dukan tsiya.
Tawagar karkashin jagorancin jami’in ‘yan sanda na shiyya ta SP, Yero Kuranga sun je wurin don gano gawar bayan da aka kai rahoton lamarin ofishin ‘yan sanda na Agbado. Daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 11.30 na dare lokacin da daya daga cikin abokan zamansa ya fita domin kashe janareto.
“Akwai kofofi guda uku (wadanda za su kai mu). Ya rufe dayan kusa da dakin yayin da zai fita ya bar sauran biyun a bude. Yayin da yake son cire janareto, sai suka far masa da adda kuma suka ji masa rauni. Suka nemi ya jagorance su zuwa dakin.
“Daya daga cikin ‘yan fashin ya buge ni da gindin bindigarsa a kai. Sun tattara wayoyinmu da kwamfutar tafi-da-gidanka kuma suka tafi daki na gaba. Sun tattara wayoyi daga mazauna biyu da ke wurin.
Sun so su fara tattara kayan ne lokacin da daya daga cikin mutanen ya musu. Hakan ya ba mu kwarin gwiwa kuma mu ma mun ba shi goyon baya don ya afka wa ’yan fashin. Nan take suka gudu amma mun sami damar rike daya daga cikinsu. ”
Wanda suka kama dan fashin ya musanta cewa sun kashe dan fashin, yana mai cewa ya yi amai da jini ne daga baya kuma ya mutu bayan da ya bayyana sunayen biyu na mambobin kungiyarsu. Ya kara da cewa, “Dan fashin ya fada mana cewa wasu mutane ne da ke kusa da al’ummar suka ba su bayanai game da mu. Sun raunata mu hudu. An harbi daya daga cikin abokan dakina su biyar ne kuma daya daga cikinsu na dauke da bindiga. ”
Wani wanda lamarin ya rutsa da shi ya bayyana cewa lokacin da suka kira lambar da aka samu a daya daga cikin wayoyin da aka sata, wani dan fashi ya karbe ta yana yi wa mambarsa ’yan kungiyar asiri da aka kama a yayin aikin.
Mazaunin ya ce, “Ya fada mana cewa marigayin dan fashin ba shi da wayo kuma shi ya sa ya mutu. Mun kai karar lamarin ga ‘yan sanda. Ba mu buge shi ba. Ba ya son bayyana asalin mambobin kungiyar tasa, yana cewa ya rantse (ba zai yi haka ba). Amma mun tilasta masa ya ambace su. Ya yi amai da jini ya mutu bayan ya ambaci sunaye biyu. ”
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda a jihar, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kara da cewa babu wanda aka kama. Ya ce, “Mun samu labarin cewa daya daga cikin ‘yan fashin an buge shi har lahira kuma tawagar ’yan sanda sun garzaya zuwa wurin. An samu gawarsa a wurin lokacin da ‘yan sanda suka isa wurin. ‘Yan fashin sun ji wa wadanda suka cutar rauni.”