• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
18 hours ago
in Labarai
0
Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya wadda a ƙiyasi take da yawan al’umma ƙasa da miliyan 230 a Agsuta 2024, ta na da adadin matasa miliyan 160 wato kashi 70 na al’ummar ƙasar.

Ranar 12 ga watan Agusta a kowace shekara Majalisar ɗinkin ɗuniya ta keɓe musamman domin tunawa da ranar matasa a duniya waɗanda ake gani da kallo a matsayin ginshiƙin ci-gaban al’umma, jakadun zaman lafiya da ayyuka nagari.

Majalisar ɗinkin ɗuniya ta keɓe ranar ne domin bitar makomar matasa, ƙarfafa masu da zaburar da su wajen gudanar da ayyukan ci-gaban ƙasa tare da nazarin ƙalubalen da ya dabaibaye su tare da tarnaƙi ga ci-gaban rayuwar su da ma hanyoyin magance su.

A shekaru aru- aru da suka gabata a na gani da kallon matasa na da muhimmiyar rawar takawa wajen ci-gaban ƙasa da hoɓɓasar ƙwazo wajen taimakawa al’umma ba tare da gajiya ko ƙosawa ba.

  • Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul
  • An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

An shaidi matasa a matsayin ƙashin bayan ci- gaban ko wace irin al’umma ta fuskoki da ɓangarori da dama waɗanda kan jajirce tare da saɗaukar da kai ga yin aiki tuƙuru domin sauke kowane irn nauyi da aka ɗora masu da hannu biyu.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Sai dai girma, kima da ɗaukakar da matasa ke da ita ga al’umma ta ja baya ƙasa sosai a bisa ga yadda rayuwarsu ke iyo da ninƙaya a kogin  zubar da mutunci ta hanyar aiwatar da abubuwan da ke da alamar ayar tambaya.

Matasa da dama a yau ba su ganin kowa da gashi, ba su girmama kowa, ba su ganin mutuncin kowa, ba su daraja kowa ballantana har a tsawata masu ko a ba su shawara da ɗora su kan hanyar yadda za su daidaita rayuwar su daga gurɓatacciyar hanya zuwa madaidaiciyar hanya.

Abin takaici ne da matuƙar damuwa yadda matasa suka gurɓata rayuwarsu mamakon amfani da lokaci da damar da suke da ita amma sai suka zaɓi biyewa ruɗin abokai da son zuciya wajen aikata abubuwan da ba su kamata ba.

Al’ummar Arewacin ƙasar nan da aka shaida da tarbiya, kamun- kai, mutunci da sanin ya kamata, a yau an wayi gari sun ɗauki gurɓatattun halayen da suka mayar da su marasa tarbiya. 

Rashin kulawar iyaye, malamai, shugabanni da dukkanin masu da tsaki ga sanya idanu ga yadda ƴaƴansu ke gudanar da rayuwar su babbar matsala ce mai zaman kan ta da ta taimaka wajen gurɓacewar rayuwar matasa.

Iyaye da dama na sakaci wajen kulawar musamman ga tarbiyar ƴaƴansu ta hanyar rashin saka idanu sosai ga yadda ƴaƴan ke gudanar da rayuwar su, abokan da suke hulɗa, wuraren da suke zuwa, binciken wayoyin su, suturar da suke saka wa da sauransu.

Idan da iyaye suna bayar da cikakkiyar kulawa ga kula da tarbiyar ƴaƴansu ta hanyar bin diddigin su a kai- a- kai da zai yi wahala a riƙa kuka a yau a yadda tarbiyar matasa ta sukurkurce.

Matasan Arewa a yau sun zama abin nunawa a bisa ga yadda tarbiyar su ta yi faɗuwar baƙar tasa, lamariin da al’ummar yankin ke kuka da kokawa musamman bisa ga rashin sanin makomar rayuwar matasa a shekaru masu zuwa.

A halin yanzu tarbiyar matasa maza da mata na fuskantar mummunar barazana da ke buƙatar iyaye, shugabanni, malamai da dukkanin masu ruwa da tsaki su tashi tsaye domin yi wa tufkar hanci tun kafin a makara wajen shawo kan bahaguwar matsalar.

Canjin zamani, kwaikwayon ɗabi’un rayuwar Turawa da kwaɗayi sun taka kuma suna ci-gaba da taka muhimmiyar rawa wajen gurɓacewar tarbiyar matasa a wannan zamanin.

Karuwanci, hulɗa da abokan banza, sharholiya da baɗala, shaye- shayen kayen maye, amfani da kafafen sada zumunta na zamani, kallon fina- finan banza, wayoyin hannu, ƙungiyoyin asiri, neman jinsi tsakanin mata da maza a baƙaƙen ɗabi’un namiji da namiji da mace da mace da sauran ayyukan fitsara lamba ɗaya abubuwa ne da ke tsunduma matasa a kogin da- na- sani 

Haka ma jahilci, talauci, kwaɗayi da neman abin duniya ido rufe da sauransu matsaloli ne da idan matasa ba su tashi tsaye haiƙan suka yaƙe su ba, to za su kai su su baro a lokacin da za su fahimci sun makaro sun makaro.

Bugu da ƙari kafafen sada zumunta na soshiyal midiya na kan gaba-gaba wajen bayar da gagarumar gudunmuwa wajen gurɓata tarbiyar matasa ta yadda matasa maza da mata ke aiwatar da abubuwan da tamkar ba su da mafaɗi.

Shigar banza ta hanyar tallata tsiraici, furta kalaman da ko kare ba zai ci ba, karuwancin yanar gizo, kalwanci tsakanin mata da maza abubuwa ne da matasa a yau ke cin karen su ba babbaka a dandalin soshiyal midiya.

Shafukan soshiyal midiya a yau a cike kuma a gurɓace suke da shafukan karuwai, ƴan daudu, ƴan luwaɗi da ƴan maɗigo waɗanda a fili suke tallata hajar su ga abokan harka wanda hakan babbar illa ce kuma babban ƙalubale ga tarbiyar matasa.

Haka ma yadda al’ummar Arewa ke gudanar da bukukuwan aure a wannan zamanin ya nuna a fili irin girman lalacewar da tarbiya ta yi a yankin a bisa ga yadda mata ke baje- kolin tsiraicin su a shigar banza wadda amarya ke jagoran ta.

Baƙuwar al’adar ranar ƙauyawa da aka fito da ita wadda a wajen bukukuwa a Arewa rana ce ta musamman da ƴan mata ke shigar fitsara da raye- rayen baɗala tamkar a ƙasar arna lamari ne da tuni gwamnatoci a Arewa suka fara ɗaukar mataki.

Gwamnatin Kano ta kasance ta farko wajen haramta ranar ƙauyawa a bukukuwan da al’ummar jihar ke yi a bisa ga illa, baɗala da matsalolin da ranar ke haifarwa musamman zubar da mutunci da darajar kyawawan al’adun ƙasar Hausa.

Bugu da ƙari sabuwar ɗabi’ar ‘saka hannu’ da matasa ƴan manyan makarantu ke yi a bisa ga murnar kammala karatu babbar matsala ce ga tarbiyar matasa. Matasan maza da mata kan yi rubutun saka hannu da maka a riguna da hijaban ƴan mata a ranar da suka kammala karatu tare da taɓa ƙirji da sauran sassan jikin matan.

Sabon salon na saka hannu a yanzu ya ɓulla har a makarantun sakandire wanda hakan babbar matsala ce da wasu gwamnatocin suka hango suka kuma haramta ɗabi’ar bakiɗaya a makarantu.

A bisa ga wannan matsalar da illarta, kwanan nan a wannan watan na Yuli gwamnatocin jihohin Sakkwato da Yobe suka bayar da sanarwar haramta murnar ‘saka hannu’ a dukkanin makarantun sakandire a jihohin biyu, matakin da ya samu yabo daga al’ummar ciki da wajen jihohin tare da kira ga sauran jihohi da su yi koyi.

Jama’a da dama na ganin gurɓatacciyar rayuwar da matasa suka ɗauka a matsayin wayewa a wannan zamanin muddin ba a samu nasarar shawo kan ta ba, to illar da za ta haifar ga manyan gobe da ke tasowa ba ƙarama ba ce.

Binciken LEAɗERSHIP HAUSA ya nuna ƴan siyasa na da kaso mai yawa na gurɓacewar rayuwar matasa a dalilin saka su aikata mabambantan ayyukan assha da suka zama silar rasa martabar su.

ƴan siyasa da dama a yau suna amfani da matasa wajen saka su a harkokin bangar siyasa, ba su kuɗin maye ko kayan maye, figar gashin kazar wannan da fashin ƙwan kazar wancan, tayar da hayaniya a wajen taron waccan jam’iyyar, ƙone ofishin ɗaya jam’iyyar da ma illata abokan adawa.

Abin damuwa ne yadda jam’iyyun siyasa a ƙasar nan ke ƙarfafa  harkokin bangar siyasa a dukkanin tarukan yekuwar neman zaɓen su a inda a kan ga matasa cike da motoci da babura a cikin shigar banza ɗauke da kowane iirin nau’i na miyagun makamai

A cewar Mainasara Giɗaɗo “yan siyasar da ke amfani da matasa wajen bangar siyasa gabanin zaɓe, galibi bayan samun nasara su kan watsar da matasan a kondon shara ba tare da assasa shiraruwan tallafawa rayuwarsu ba wanda ya kamata matasan su yi wa kan su karatun ta- natsu ta hanyar ƙauracewa waɗanda ba su damu da inganta rayuwar su ba.”

Ya ce “Matasa da dama a yau waɗanda ya kamata su himmatu wajen neman ilimi da aiki da shi tare da gudanar da sana’o’i nagari, sun banzantar da lokacin su ga shiga sabgogin da suke zubar da kima da mutuncin su ga al’umma.”

A yau matasan ƴan mata sun dabaibaye rayuwarsu da rashin tarbiya, sharholiya da baɗala da mayar da fitsara tamkar wani ado na musamman lamarin da ya zama babban ƙalubale gare su wajen samun mazaje nagari.

Masu fashin baƙin lamurran yau da kullum kan bayyana cewar kasuwar kamilallun ƴan mata nagari waɗanda suka nesanta kan su da ayyukan baɗala da abota da ƙawayen banza ta fi tashi a sauƙin neman aure akasin ƴan matan da suka yi wa kan su baƙin fentin fitsara da ke kasa samun mazaje cikin sauƙi.

A gidan aure rahotanni sun nuna yadda ƴan mata da dama ke kasa sauke nauyin gida da ya rataya a wuyansu domin galibin matasan wannan zamanin a bayyane suke bayyanawa mazaje su ba za su iya yi masu girki ba ballantana gudanar da wasu aikace- aikacen gida da suka wajaba wanda duka rashin tarbiya ne ya haddasa hakan.

A ra’ayin wani matashi, Ayuba Bello Okimo ya bayyana cewar rayuwar matasa ta na cikin babban ƙalubale a kan yadda suka tsunduma a harkokin zubar da mutunci.

Ya ce “Tabbas rayuwar matasa ta na cikin babban ƙalubale domin matasa sun tsunduma a harkokin banza da shaye- shaye gadan gadan wanda yayi tasiri wajen gurɓacewar tarbiyar matasa.”

“Wannan matsalar a yanzu har ta kai matasa na ganin matashin da ba ya yi bai waye ba, kazalika matasa a wannan lokacin suna son kuɗi ta kowane hali da son yin rayuwa mai kyau amma sai dai ba sa son neman na kai da aikin wahala, don haka lallai- lallai akwai ƙalubale sosai.”

Ya ce “ɗukkan al’ummar da Allah ya arzirta su da matasa a na cewa sun yi dace domin duk abin da ya tunkaro su za su nuna ƙarfi da zarra irin ta matasa domin cinma nasara. Tabbas Arewacin Nijeriya Allah ya albarkace mu da matasa, amma sai dai kash waɗannan matasan maimakon su kasance matasa wadanda za a yi alfahari da su sai suka kasance waɗanda ake kuka da su, sabo da an riga da an gurɓata tunani da hankalinsu, ta hanyar ayyukan banza da shaye- shaye.”

“Wasu daga cikin azzaluman shugabanni waɗanda ba sa kishin matasan ballantana son ci-gabansu, su ke saya musu kayan shaye shaye suna sha domin kawar da hankalinsu domin aiwatar da ayyukan da suka ɗora su a kai a lokacin da  su kuma ƴayansu suna makarantun ƙwarai a ciki da wajen ƙasa suna karatu.”

Ya ce wajibi ne matasa su yi wa kan su faɗa su yi karatun ta- natsu domin ceto goben su ta yadda za a yi alfahari da su ko bayan rai ya yi halinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MatasaTarbiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

Next Post

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

6 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

7 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

12 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

14 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

14 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

17 hours ago
Next Post
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.