• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru 3 bayan barkewar annobar cutar numfashi ta COVID-19 a duniya, kasar Sin tana mayar da jama’arta da rayukansu a gaban kome. Ta kuma kyautata matakan yaki da cutar bisa lokaci da yanayin da ake ciki. Tana kuma raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasa da kuma dakile yaduwar cutar a lokaci guda, tare da kiyaye rayuka da lafiyar jama’arta yadda ya kamata.

Daga karshen shekarar 2019 zuwa watanni 6 na farkon shekarar 2020, kasar Sin ta gano barkewar annobar a kan lokaci, inda ta tsai da kuduri mai muhimmanci na daukar matakin kulle a birnin Wuhan nan take ba tare da bata lokaci ba, lamarin da ya hana yaduwar cutar zuwa sauran sassan kasar, ta yadda Sin ta tabbatar da daidaiton dakile da kandagarkin cutar a duk fadin kasar, da yin iyakacin kokarin rage asarar rayukan jama’arta. Daga watanni 6 na farkon shekarar 2020 zuwa karshen shekarar 2022, kasar Sin ta yi wa al’ummarta mafi yawa a duniya allurar rigakafin cutar kyauta cikin gajeren lokaci, lamarin da ya sa yawan masu kamuwa da cutar da kuma yawan mutuwar mutane sakamakon cutar dukkansu suka fi kankanta a duniya.

A yayin da kasar Sin take daidaita matsaloli da dama, har kullum tana mara wa kasashen duniya baya wajen yaki da cutar ta COVID-19. Ta samar wa kasashe 153 da kungiyoyin kasa da kasa 15 daruruwan biliyoyin kayayyakin kandagarkin cutar. Ta kuma samar wa kasashe da yankuna fiye da 180 da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 10 fasahohin dakile da kandagarkin cutar da ba da jinya da kiwon lafiya. Kana kuma, kasar Sin ta tura kungiyoyin masana ilmin lafiya 37 zuwa kasashe 34, a kokarin samar da kyawawan fasahohinta na yaki da cutar ba tare da rufa-rufa ba. Har ila yau, kasar Sin ta samar wa kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 120 alluran rigakafin cutar fiye da biliyan 2.2, hakan ya sa kasar Sin zama kasar da ta fi samar wa kasashen duniya alluran.

Tun daga watan Nuwamban shekarar 2022 da ta gabata, kasar Sin ta rika kyautata matakan yaki da cutar, bisa manufar “kiyaye lafiya da magance samun yawan wadanda ke fama da cutar mai tsanani”, ta kuma samu nasara cikin kankanin lokaci, inda aka yi wa mutane fiye da miliyan 200 jinya, tare da ceton wadanda ke fama da cutar mai tsanani kimanin dubu 800. Lamarin da ya sa yawan mutanen da suka mutu sakamakon cutar ya fi kankanta a duk duniya. Kasar Sin ta samu gagarumar nasarar yaki da cutar ta COVID-19, tare da yin abin al’ajabi a tarihin dan Adam. (Tasallah Yuan)

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Takarar Majalisar Tarayya Na PDP A Kano Municipal, Da’awah Ya Rabawa Dalibai 500 JAMB

Next Post

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

2 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

4 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

5 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

6 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

7 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

9 hours ago
Next Post
Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.