• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbatar Da Daidaito Da Cin Moriyar Juna Suna Cikin Babban Ruhin Shawarar BRI

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tabbatar Da Daidaito Da Cin Moriyar Juna Suna Cikin Babban Ruhin Shawarar BRI
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI), wata shawara ce ta hadin gwiwar kasa da kasa, da kasar Sin ta gabatar a shekarar 2013. Zuwa yanzu, kasar ta riga ta kulla takardun hadin gwiwa tare da kasashe fiye da 150, da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 30, da gudanar da ayyukan hadin gwiwa fiye da 3000, da janyo jarin da ya kai dalar Amurka fiye da triliyan 1, duk a karkashin shawarar BRI.

A yau, an yi bikin kaddamarwar taron koli na hadin gwiwar kasa da kasa a karkashin shawarar BRI karo na 3, a birnin Beijing na kasar Sin, wanda ya samu halartar manyan kusoshin kasashen fiye da 140, da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 30, ciki har da mataimakin shugaban tarayyar Najeriya Kashim Shettima.

  • Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci
  • Kasar Sin Na Fatan A Gaggauta Kawo Karshen Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

A cikin jawabin da ya gabatar a wajen bikin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada cewa, shawarar BRI ta fi dora muhimmanci kan hadin gwiwa da taimakawa juna, inda ake neman tabbatar da cin moriya da ci gaba tare.

Game da tunanin cin moriya, tare da samun ci gaba tare da shawarar BRI ta kunsa, wasu abokai su kan nuna shakku, inda sukan ce, “ Ku Sinawa kuna zuwa Najeriya ne ba domin moriyar kanku ba?” Sai dai a hakika, alfanun shawarar BRI ya riga ya fito fili sosai a Najeriya.

Misali, a jihar Lagos, akwai wani kamfanin sarrafa kayan kwalliya na shafe-shafe, wanda ke bukatar shigar da wasu sinadarai daga ketare. Sai dai ma’aikatan kamfanin sun fi damuwa, lokacin da sinadaran da suke bukata suka iso tashar jirgin ruwa ta Apapa. Ina dalili? Saboda a kan samu cunkuso a tashar Apapa, inda dimbin motocin daukar kaya ke jiran a kwashe kayayyaki daga jiragen ruwa. Ko da yake ba nisa tsakanin tasha da kamfanin, amma a kan dauki wata daya kafin a iya kai kaya zuwa kamfanin. Sai dai yanayin ya sauya, bayan da aka fara yin amfani da babbar tashar jiragen ruwa ta Lekki, wadda aka gina ta karkashin shawarar BRI. Yanzu bayan da kayan kamfanin ya iso tashar, cikin kwanaki 7 za a iya samun kayan. Ta haka, kamfanin ya samu tsimin kudin da yake kashewa, saboda ba bukatar biyan karin kudi, idan an iya fitar da kaya daga cikin tasha cikin kwanaki 14.

Labarai Masu Nasaba

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

Akwai dimbin kamfanonin da suka yi kama da wannan kamfanin da muka ambata, wadanda suka samu muhallin gudanar da ciniki mai inganci sakamakon kafuwar tashar ruwa ta Lekki. Yanzu haka sun samu kwarin gwiwar zuba karin jari a Najeriya, da daukar karin ma’aikata. Hakan shi ma ya sa yankin ciniki mai ‘yanci na Lekki, da kasashen Najeriya da Sin suka kafa cikin hadin kai bisa shawarar BRI, samun ci gaba sosai. Zuwa watan Yunin bana, akwai kamfanoni 175 da suka yi rajista a yankin, ciki har da kamfanonin Sin 73, da kamfanonin kasa da kasa 43. Kana a farkon watannin 6 na bana, kamfanonin da ke cikin yankin sun shigar da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 28, da fitar da kayan na dala miliyan 70 zuwa ketare. Ta wannan yanayi na sa kaimi ga masana’antu da ciniki, ana sa ran ganin tashar Lekki ta samar da kudin shiga har dala biliyan 361, da guraben aikin yi dubu 170 ga kasar Najeriya, cikin shekaru 45 masu zuwa.

Daga misalin tashar jirgin ruwa ta Lekki, za mu iya ganin yadda ake gudanar da hadin gwiwa a karkashin shawarar BRI: Da farko ana gina kayayyakin more rayuwa don tabbatar da hadewar yankuna daban daban, sa’an nan za a samu kyautatuwar muhallin kasuwanci, da sa kaimi ga ciniki da zuba jari, ta yadda za a tabbatar da ci gaban tattalin arzikin daukacin yankin da ake ciki. Ta wannan hanya, Sinawa za su iya samun riba bisa jarin da suka zuba, yayin da mutanen Najeriya su ma za su samu biyan bukatarsu, ta raya kasa, da kyautata zaman rayuwa.

Sai dai, a ko ina, ba za a rasa mutane masu nuna shakku ba. Kamar yadda wasu kan ce, “Shawarar BRI na da kyau, amma tana sanya kasashen Afirka cikin tarkon bashi”. Sai dai idan an kara yin bincike kan maganar, za a gane cewa ba ta da tushe ko kadan. Idan shawarar BRI na da wannan mummunar illa, anya za a ci gaba da samun kasashe fiye da 150 da suke son shiga cikin ta?

A hakika, alkaluman bankin duniya sun nuna cewa, masu jari na kasashen yamma sun fi bin kasashen Afirka bashi, yayin da bashin da kasar Sin ta bayar bai wuce kashi 17% kacal ba, cikin dukkan basussukan da kasashen Afirka suka ci. Ban da haka, kasar Sin ta dade tana samar da rancen kudi dake bukatar biyan ruwa kadan, ga kasashe marasa karfi dake nahiyar Afirka, gami da kokarin shiga shawarar daina biyan bashi ta kungiyar G20, inda ta kulla yarjejeniyar daina biyan bashi, ko kuma cimma matsaya a wannan fanni, tare da kasashe 19 dake nahiyar Afirka. Kana wani abun da ya fi muhimmanci shi ne, kasar Sin ta dade tana kokarin tattaunawa tare da sauran kasashe, kan yadda za su iya yin hadin gwiwa bisa matsayi na daidai wa daida. Saboda haka, rancen da kasar Sin ta samar, ba zai yi kama da rancen kasashen yamma ba, wanda ya zama abin da suke yin amfani da shi wajen shawo kan kasashen Afirka.

Su kasashen yamma su kan nuna girman kai, yayin da suke hulda da kasashe masu tasowa, inda suke ikirarin cewa “Gaskiya tana hannuna.” Wannan tunani an gaje shi ne daga lokacin mulkin mallaka. A nata bangare, kasar Sin ba ta da wannan tunani na ‘yan mulkin mallaka. Saboda ta kasance daya daga cikin kasashe masu tasowa, inda take koyon fasahohin kasashen yamma, da lalubo turbar raya kasa ta kai, sa’an nan sannu a hankali, ta kai matsayi na yanzu. Saboda haka kasar Sin tana iya zama cikin daidaito tare da sauran kasashe masu tasowa, da son tattaunawa tare da su, don neman hanyar da za a bi, a kokarin tabbatar da ingancin hadin gwiwar da ake yi karkashin shawarar BRI. Wannan ne ma ya sa shugaba Xi Jinping, ya mai da kyautata tsarin hadin gwiwa karkashin shawarar BRI wani aiki mai muhimmanci, cikin jawabin da ya bayar a yau. Wato a tattauna kafin a aiwatar da wani mataki, da yin gyara a kai a kai, don mai da shawarar BRI wani abun da zai tabbatar da cin moriya tare da samun ci gaba tare, kuma ta haka ne ake tabbatar da kyakkyawar makoma ga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IMFShawarar ziri dayaXi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Rukunin Al’umma

Next Post

Wike Zai Rushe Wani Bangare Na Babban Masallacin Kasa

Related

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

31 minutes ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

2 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

3 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

4 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

23 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

24 hours ago
Next Post
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

Wike Zai Rushe Wani Bangare Na Babban Masallacin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.