• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani manazarci a kasar Afrika ta Kudu, David Monyae ya ce, yayin da kasar Sin ta kama sabuwar hanyar gina kasa ta zamani bisa tsarin gurguzu ta hanyar zamanintar da kanta, ya kamata kasashe masu tasowa na Afrika da sauran sassan duniya, su yi amfani da damar da Sin ta samar, ta zamanantar da kansu bisa yanayinsu na cikin gida.

David Monyae wanda shi ne daraktan cibiyar nazarin harkokin Afrika da Sin ta jami’ ar Johannesburg, ya bayyanawa kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu na karfin tattalin arziki a duniya, ya sauya dadadden ra’ayin da ake da shi cewa, hanyar zamanintarwa ta yammacin duniya ita ce daidaitacciyar hanyar samun ci gaba a duniya.

Ya ce, zamanintarwa irin ta kasar Sin na da damar karfafawa da yin tasiri a sauran sassan duniya, musamman tsakanin kasashe masu tasowa.

Ya kara da cewa, nasarorin da Sin ta samu a baya-bayan nan wajen fatattakar talauci da samun ci gaban tattalin arziki, sun burge shi.

Da yake bayyana nasarar da Sin ta samu na fatattakar talauci a matsayin nasara ta bai daya ga duniya maimakon nata ita kadai, David Monyae ya kara da cewa, kasar Sin ta cimma muradi na farko cikin muradun ci gaba masu dorewa na MDD da ake son cimmawa zuwa shekarar 2030, shekaru 10 kafin lokacin da aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Har ila yau, ya ce ya kamata kasashe masu tasowa su samu kwarin gwiwa tare da zamanantar da kansu ta hanyar da ta dace da yanayi da tarihi da zaman takewa da tsarin tattalin arzikinsu. (Fa’iza)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

Next Post

Sin Ba Abokiyar Gabar Amurka Ba Ce

Related

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi
Daga Birnin Sin

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

2 hours ago
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

10 hours ago
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin
Daga Birnin Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

11 hours ago
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

12 hours ago
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

13 hours ago
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka
Daga Birnin Sin

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

14 hours ago
Next Post
Sin Ba Abokiyar Gabar Amurka Ba Ce

Sin Ba Abokiyar Gabar Amurka Ba Ce

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.