• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafarnuwa Ma Barazana Ce?

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Tafarnuwa Ma Barazana Ce?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’a, me za ku ce idan kun ji an ce “tafarnuwa za ta iya haifar da barazana ga tsaron kasa”? Tabbas za ku dauki zancen a matsayin abin dariya. 

 

Sai dai an ji zancen ne a bakin wani babban jami’in kasar Amurka. Dan majalisar dattawan Amurka, Rick Scott a baya-bayan nan ya fitar da wata sanarwa yana mai cewa, tafarnuwa da aka yi nomanta a kasar Sin tana da “babbar barazana” ga tsaron kasar Amurka a fannin samun abinci mai inganci, ya kuma yi kira da a kaddamar da bincike bisa aya ta 301 ta dokar ciniki ta shekarar 1974 ta kasar Amurka. Kana majalisar wakilan Amurka ta yi nazari tare da zartas da “dokar ba da izinin tsaron kasa ta sabuwar shekarar kasafin kudi ta shekarar 2025”, wadda kuma ta hada da tanade-tanade da ke bukatar shagunan sojin Amurka hana sayar da tafarnuwar kasar Sin.

  • Me Ke Kawo Zargi Tsakanin Wadanda Suke Gab Da Su Yi Aure?
  • Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

Tafarnuwa ba ta taba tunanin za ta iya yin babbar barazana ga Amurka ba. Amma ba a rasa jin irin wadannan abubuwa cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. Daga shigowa da motoci, da jirgi marasa matuki, da na’urorin daga kaya, kai har zuwa tafarnuwa, tamkar dukkansu na iya “haifar da barazana ga tsaron kasar Amurka”. Amurka ta kusan haukacewa domin “tsoron kasar Sin”.

 

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Sai dai al’ummar duniya suna gano cewa, Amurka na fakewa ne da batun “tsaron kasa” wajen daukar matakan kariyar ciniki, kuma tana neman dakile bunkasuwar kasar Sin. In mun dauki misali da tafarnuwa wadda ke ba Mr. Scott tsoro, kasar Sin na daga cikin kasashen da suke yawan samar da tafarnuwa, da kuma fitar da su zuwa ketare, ita kuma kasa ce da ta fi yawan fitar da tafarnuwa ga kasar Amurka, a cikin gomman shekaru da suka wuce, sau da dama kasar Amurka ta kara haraji a kan tafarnuwa da take shigowa daga kasar Sin bisa dalili na wai “kin yarda da sayar da kayayyaki da yawa da farashi mai matukar rahusa”, kuma Mr.Scott na daga cikin wadanda ke sa kaimin daukar matakin.

 

A wasakun da ya aikawa jami’an gwamnatin kasar Amurka, Mr. Scott ya ce wai “kasar Sin ta shuka tafarnuwa da gurbataccen ruwa”, yana mai bayyana damuwarsa game da yadda ake yawan shigowa da tafarnuwa daga kasar Sin. Amma a hakika, kasar Sin na da tsari mai tsanani da ake bi wajen gudanar da ayyukan gona, ciki har da noman tafarnuwa, idan da gaske ne tafarnuwar da ta samar na da matsala, to, hukumomin kwastan na kasar Amurka da ke kula da ayyukan duba ingancin kayayyakin da ake shigowa da su za su gano su, sam ba za a yarda da shigowar tafarnuwar kofar gidan Amurka ba.

 

Sanin kowa ne, Amurka ta sha yin kiran “’yancin takara”, da “’yancin ciniki” a yayin da take zargin wasu kasashe da rashin ’yanci a kasuwanninsu. Amma yayin da kasashe masu tasowa ke dada bunkasa, tare da cimma nasarori wajen kirkire-kirkiren fasahohi, Amurka ita kanta kuma masana’antunta na raguwa, nan da nan sai Amurka ta manta da ‘yancin ciniki da na takara, kuma ta dauki matakai iri iri na dakile abokan takararta, da ci gaban sauran kasashe.

 

Sai dai a zamanin da muke ciki na dunkulewar tattalin arzikin duniya, sassan kasa da kasa sun kasance suna cude-ni-in-cude-ka. Duk wata nasarar kirkire-kirkire ta kan samu ne bisa hadin gwiwar sassan duniya daban daban. Fakewa da batun tsaron kasa don siyasantar da harkokin tattalin arziki, da ciniki, da kimiyya da fasaha, ba zai haifar da komai ba, illa ya lalata tsarin samar da kayayyaki na duniya, har ma ya lahanta moriyar kai.

 

Shawara ga kasar Amurka ita ce ta mai da hankali a kan gano bakin zaren warware matsalolin da take fuskanta, kuma ta kalli ci gaban sauran kasashe yadda ya kamata, tare da rungumar hadin gwiwar kasa da kasa, hakan zai kawar da damuwarta game da kasar Sin, da ba ta damar gano hanyar kara raya kanta. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

Next Post

Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

12 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

3 days ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Next Post
Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.