• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafarnuwa Ma Barazana Ce?

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Tafarnuwa

Jama’a, me za ku ce idan kun ji an ce “tafarnuwa za ta iya haifar da barazana ga tsaron kasa”? Tabbas za ku dauki zancen a matsayin abin dariya. 

 

Sai dai an ji zancen ne a bakin wani babban jami’in kasar Amurka. Dan majalisar dattawan Amurka, Rick Scott a baya-bayan nan ya fitar da wata sanarwa yana mai cewa, tafarnuwa da aka yi nomanta a kasar Sin tana da “babbar barazana” ga tsaron kasar Amurka a fannin samun abinci mai inganci, ya kuma yi kira da a kaddamar da bincike bisa aya ta 301 ta dokar ciniki ta shekarar 1974 ta kasar Amurka. Kana majalisar wakilan Amurka ta yi nazari tare da zartas da “dokar ba da izinin tsaron kasa ta sabuwar shekarar kasafin kudi ta shekarar 2025”, wadda kuma ta hada da tanade-tanade da ke bukatar shagunan sojin Amurka hana sayar da tafarnuwar kasar Sin.

  • Me Ke Kawo Zargi Tsakanin Wadanda Suke Gab Da Su Yi Aure?
  • Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

Tafarnuwa ba ta taba tunanin za ta iya yin babbar barazana ga Amurka ba. Amma ba a rasa jin irin wadannan abubuwa cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. Daga shigowa da motoci, da jirgi marasa matuki, da na’urorin daga kaya, kai har zuwa tafarnuwa, tamkar dukkansu na iya “haifar da barazana ga tsaron kasar Amurka”. Amurka ta kusan haukacewa domin “tsoron kasar Sin”.

 

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Sai dai al’ummar duniya suna gano cewa, Amurka na fakewa ne da batun “tsaron kasa” wajen daukar matakan kariyar ciniki, kuma tana neman dakile bunkasuwar kasar Sin. In mun dauki misali da tafarnuwa wadda ke ba Mr. Scott tsoro, kasar Sin na daga cikin kasashen da suke yawan samar da tafarnuwa, da kuma fitar da su zuwa ketare, ita kuma kasa ce da ta fi yawan fitar da tafarnuwa ga kasar Amurka, a cikin gomman shekaru da suka wuce, sau da dama kasar Amurka ta kara haraji a kan tafarnuwa da take shigowa daga kasar Sin bisa dalili na wai “kin yarda da sayar da kayayyaki da yawa da farashi mai matukar rahusa”, kuma Mr.Scott na daga cikin wadanda ke sa kaimin daukar matakin.

 

A wasakun da ya aikawa jami’an gwamnatin kasar Amurka, Mr. Scott ya ce wai “kasar Sin ta shuka tafarnuwa da gurbataccen ruwa”, yana mai bayyana damuwarsa game da yadda ake yawan shigowa da tafarnuwa daga kasar Sin. Amma a hakika, kasar Sin na da tsari mai tsanani da ake bi wajen gudanar da ayyukan gona, ciki har da noman tafarnuwa, idan da gaske ne tafarnuwar da ta samar na da matsala, to, hukumomin kwastan na kasar Amurka da ke kula da ayyukan duba ingancin kayayyakin da ake shigowa da su za su gano su, sam ba za a yarda da shigowar tafarnuwar kofar gidan Amurka ba.

 

Sanin kowa ne, Amurka ta sha yin kiran “’yancin takara”, da “’yancin ciniki” a yayin da take zargin wasu kasashe da rashin ’yanci a kasuwanninsu. Amma yayin da kasashe masu tasowa ke dada bunkasa, tare da cimma nasarori wajen kirkire-kirkiren fasahohi, Amurka ita kanta kuma masana’antunta na raguwa, nan da nan sai Amurka ta manta da ‘yancin ciniki da na takara, kuma ta dauki matakai iri iri na dakile abokan takararta, da ci gaban sauran kasashe.

 

Sai dai a zamanin da muke ciki na dunkulewar tattalin arzikin duniya, sassan kasa da kasa sun kasance suna cude-ni-in-cude-ka. Duk wata nasarar kirkire-kirkire ta kan samu ne bisa hadin gwiwar sassan duniya daban daban. Fakewa da batun tsaron kasa don siyasantar da harkokin tattalin arziki, da ciniki, da kimiyya da fasaha, ba zai haifar da komai ba, illa ya lalata tsarin samar da kayayyaki na duniya, har ma ya lahanta moriyar kai.

 

Shawara ga kasar Amurka ita ce ta mai da hankali a kan gano bakin zaren warware matsalolin da take fuskanta, kuma ta kalli ci gaban sauran kasashe yadda ya kamata, tare da rungumar hadin gwiwar kasa da kasa, hakan zai kawar da damuwarta game da kasar Sin, da ba ta damar gano hanyar kara raya kanta. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Tafarnuwa

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.