ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafarnuwa Ma Barazana Ce?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Tafarnuwa

Jama’a, me za ku ce idan kun ji an ce “tafarnuwa za ta iya haifar da barazana ga tsaron kasa”? Tabbas za ku dauki zancen a matsayin abin dariya. 

 

Sai dai an ji zancen ne a bakin wani babban jami’in kasar Amurka. Dan majalisar dattawan Amurka, Rick Scott a baya-bayan nan ya fitar da wata sanarwa yana mai cewa, tafarnuwa da aka yi nomanta a kasar Sin tana da “babbar barazana” ga tsaron kasar Amurka a fannin samun abinci mai inganci, ya kuma yi kira da a kaddamar da bincike bisa aya ta 301 ta dokar ciniki ta shekarar 1974 ta kasar Amurka. Kana majalisar wakilan Amurka ta yi nazari tare da zartas da “dokar ba da izinin tsaron kasa ta sabuwar shekarar kasafin kudi ta shekarar 2025”, wadda kuma ta hada da tanade-tanade da ke bukatar shagunan sojin Amurka hana sayar da tafarnuwar kasar Sin.

ADVERTISEMENT
  • Me Ke Kawo Zargi Tsakanin Wadanda Suke Gab Da Su Yi Aure?
  • Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

Tafarnuwa ba ta taba tunanin za ta iya yin babbar barazana ga Amurka ba. Amma ba a rasa jin irin wadannan abubuwa cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. Daga shigowa da motoci, da jirgi marasa matuki, da na’urorin daga kaya, kai har zuwa tafarnuwa, tamkar dukkansu na iya “haifar da barazana ga tsaron kasar Amurka”. Amurka ta kusan haukacewa domin “tsoron kasar Sin”.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Sai dai al’ummar duniya suna gano cewa, Amurka na fakewa ne da batun “tsaron kasa” wajen daukar matakan kariyar ciniki, kuma tana neman dakile bunkasuwar kasar Sin. In mun dauki misali da tafarnuwa wadda ke ba Mr. Scott tsoro, kasar Sin na daga cikin kasashen da suke yawan samar da tafarnuwa, da kuma fitar da su zuwa ketare, ita kuma kasa ce da ta fi yawan fitar da tafarnuwa ga kasar Amurka, a cikin gomman shekaru da suka wuce, sau da dama kasar Amurka ta kara haraji a kan tafarnuwa da take shigowa daga kasar Sin bisa dalili na wai “kin yarda da sayar da kayayyaki da yawa da farashi mai matukar rahusa”, kuma Mr.Scott na daga cikin wadanda ke sa kaimin daukar matakin.

 

A wasakun da ya aikawa jami’an gwamnatin kasar Amurka, Mr. Scott ya ce wai “kasar Sin ta shuka tafarnuwa da gurbataccen ruwa”, yana mai bayyana damuwarsa game da yadda ake yawan shigowa da tafarnuwa daga kasar Sin. Amma a hakika, kasar Sin na da tsari mai tsanani da ake bi wajen gudanar da ayyukan gona, ciki har da noman tafarnuwa, idan da gaske ne tafarnuwar da ta samar na da matsala, to, hukumomin kwastan na kasar Amurka da ke kula da ayyukan duba ingancin kayayyakin da ake shigowa da su za su gano su, sam ba za a yarda da shigowar tafarnuwar kofar gidan Amurka ba.

 

Sanin kowa ne, Amurka ta sha yin kiran “’yancin takara”, da “’yancin ciniki” a yayin da take zargin wasu kasashe da rashin ’yanci a kasuwanninsu. Amma yayin da kasashe masu tasowa ke dada bunkasa, tare da cimma nasarori wajen kirkire-kirkiren fasahohi, Amurka ita kanta kuma masana’antunta na raguwa, nan da nan sai Amurka ta manta da ‘yancin ciniki da na takara, kuma ta dauki matakai iri iri na dakile abokan takararta, da ci gaban sauran kasashe.

 

Sai dai a zamanin da muke ciki na dunkulewar tattalin arzikin duniya, sassan kasa da kasa sun kasance suna cude-ni-in-cude-ka. Duk wata nasarar kirkire-kirkire ta kan samu ne bisa hadin gwiwar sassan duniya daban daban. Fakewa da batun tsaron kasa don siyasantar da harkokin tattalin arziki, da ciniki, da kimiyya da fasaha, ba zai haifar da komai ba, illa ya lalata tsarin samar da kayayyaki na duniya, har ma ya lahanta moriyar kai.

 

Shawara ga kasar Amurka ita ce ta mai da hankali a kan gano bakin zaren warware matsalolin da take fuskanta, kuma ta kalli ci gaban sauran kasashe yadda ya kamata, tare da rungumar hadin gwiwar kasa da kasa, hakan zai kawar da damuwarta game da kasar Sin, da ba ta damar gano hanyar kara raya kanta. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Tafarnuwa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
Tafarnuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara
  • Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa
  • Sulaiman
    Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?
  • Sulaiman
    Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

Motoci Kirar Kamfanin Kasar Sin Na Samun Karin Karbuwa A Kasar Ghana

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026
Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

September 12, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa

September 12, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.