• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cikin jerin bayanai daga ‘yan jaridar Afirka, ‘yar Ghana Elizabeth Ohene ta yi rubutu game da irin rikicin da ake yi kafin binne shugabannin Afirka.

“Ba ni da tabbas ko zan iya ba da wani taKadirin zance, amma ni ban taba sanin cewa kasancewar mutum shugaban wata Kasa a Afirka zai iya haddasa rigima a Kabarinsa ba idan ya rasu.

  • Masanin Masar: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Wani “Karfi Ne Dake Ingzia Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Na yi ta bin rikicin da ake yi game da inda za a binne Tsohon Shugaban Kasar Angola José Eduardo dos Santos, wanda ya rasu a Sifaniya ranar 8 ga watan Yuli.

Shugaban Kasar mai-ci João Lourenço da kuma matar Dos Santos na son a mayar da gawarsa gida don yi mata jana’izar ban-girma a Kasaitacciyar maKabarta ta musamman – abin da muke gani na girmamawa ga shugabanni a Ghana.

Amma ‘yarsa mai suna Welwitschia “Tchizé” na son a yi masa jana’iza a killace kuma a binne shi a wani Kabari na musamman a Sifaniya ta yadda ‘ya’yansa za su iya ziyartarsa,” in ji ta.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

Ta ce wasu daga cikin ‘yan uwanta na goyon bayan Kudirin nata, wadanda ke fuskantar zargin cin hanci kuma za a iya kama su da zarar sun saka Kafa a Angola.

Daya daga cikin ‘ya’yan Dos Santos ya ce ba Kasar ce ke da alhakin daukar nauyin jana’izarsa ba kuma iyalinsa ne ya kamata su yanke hukunci.

Maganar cewa ko Kasa na da iko kan gawar shugabanta ba sabon abu ba ne.
An samu irin wannan lamari a Zimbabwe a 2019, lokacin da Robert Mugabe ya rasu shekara kusan biyu da suka wuce bayan ya shekara 37 a kan mulki – inda shugaba mai-ci Emmerson Mnangagwa ya kawo Karshen mulkin nasa tare da goyon bayan sojoji.

Kowa ya yi tunanin za a binne shi ne a Filin Gwaraza na Kasa ( Heroes’ Acre) da ke Birnin Harare.

Ko ma dai mene ne, shi ne ya gina Heroes’ Acre kuma ya binne da yawa daga cikin abokan gwagwarmayarsa, ciki har da Sally matarsa ta farko.

Mista Mnangagwa ya fara gina Kabari na musamman don binne jagoran neman ‘yancin, amma kuma iyalansa ba su amince da hakan ba ganin yadda aka kore shi daga mulki kuma abokan gwagwarmyarsa suka yaudare shi.

Bayan shafe makonni ana taKaddama, iyalinsa sun yi nasara kuma an binne Mista Mugabe, jagora kuma gwarzo a Zimbabwe, a Kauyensu ba tare da wani wakilin gwamnati ba.

Hatta Kenneth Kaunda – shugaban Kasa na farko bayan ‘yancin kai a Kasar Zambia kuma daya daga cikin ‘yan gwagwarmayar neman ‘yanci – bai iya samun wurin da za a binne shi ba ba tare da rikici ba.

A cewar iyalinsa, ya so a binne shi kusa da matarsa ba inda gwamnati ta tanada ba.

Zuwa yanzu dai iyalin nasa ba su yi wata jayayya ba yayin da “KK” – kamar yadda ake kiran sa da shi – na ci gaba da kwanciya a Embassy Memorial Park da ke Lusaka baban birnin Kasar.

Daga gudun hijira zuwa girmamawa
“Wadannan rikice-rikice kan gawarwaki ba sabbin abubuwa ba ne. A nan Ghana, mun saba da irin wannan.

Shugaban Kasarmu na farko Kwame Nkrumah ya rasu a Bucharest na Romania lokacin da yake jinya.
Da farko an binne shi a Conakry, Guinea bayan ya shafe lokaci yana gudun hijira a can. Daga baya aka mayar da gawarsa Ghana. An yi masa jana’izar gwamnati a Accra sannan aka binne shi a Kauyensu na Nkroful.

A lokuta daban-daban za ka dinga jin iyalansa na cewa a dawo musu da gawarsa.

A 2012, shugaban Kasarmu John Atta-Mills ya rasu yana kan mulki amma samun wurin da za a binne shi ya zama aiki.

Wasu daga cikin iyalansa sun nemi a kai gawarsa Kauyensu, sai dai ba su samu wani goyon baya ba a lokacin.

An Kyale wurin da gwamnati ta haKa a matsayin Kabarinsa saboda bai dace da shi ba. Daga baya aka mayar da shi wani wuri daban.

An tsara cewa wurin shaKatawar da aka binne shi ya zama maKabartar shugabannin Kasa.

Tun daga wannan lokaci, wani shugaban Kasar – Jerry Rwlings – yara su.
Ba kai shi wurin da aka binne Shugaba Atta-Mills kawai ba, iyalansa sun zargi gwamnati da aiwatar da hakan ba tare da izininsa ba.

An binne shi a maKabartar sojoji da ke Accra tare da yi masa jana’izar girmamawa.
‘Yan makonni da suka wuce muka yi bikin cika shekara 10 da mutuwar Atta-Mills.
Har yanzu ana cecekuce a kan kushewarsa: wane ne zai kula da ita kuma me za a rubuta a kanta.

Akwai kuma wasu daga iyalansa da ke son a tono gawarsa daga inda gwamnati ta binne shi a Accra zuwa Kuyensu don a sake binne shi.

Saboda haka ina ganin daya daga cikin matsalolin zama shugaban Kasa a Afirka ita ce ba lallai a samu wurin da za a binne mutum ba idan ya rasu,” a cewar ‘yar jaridar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Duƙufa Tabbatar Da Tsaron Iyakokin Nijeriya – CGI Isah Jere

Next Post

Yadda Za Ka Fara Sana’ar Sayar Da Data

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

24 hours ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

1 week ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

1 week ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Next Post
Yadda Za Ka Fara Sana’ar Sayar Da Data

Yadda Za Ka Fara Sana'ar Sayar Da Data

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.