• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

by Sulaiman
3 years ago
Afirka

Cikin jerin bayanai daga ‘yan jaridar Afirka, ‘yar Ghana Elizabeth Ohene ta yi rubutu game da irin rikicin da ake yi kafin binne shugabannin Afirka.

“Ba ni da tabbas ko zan iya ba da wani taKadirin zance, amma ni ban taba sanin cewa kasancewar mutum shugaban wata Kasa a Afirka zai iya haddasa rigima a Kabarinsa ba idan ya rasu.

  • Masanin Masar: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Wani “Karfi Ne Dake Ingzia Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Na yi ta bin rikicin da ake yi game da inda za a binne Tsohon Shugaban Kasar Angola José Eduardo dos Santos, wanda ya rasu a Sifaniya ranar 8 ga watan Yuli.

Shugaban Kasar mai-ci João Lourenço da kuma matar Dos Santos na son a mayar da gawarsa gida don yi mata jana’izar ban-girma a Kasaitacciyar maKabarta ta musamman – abin da muke gani na girmamawa ga shugabanni a Ghana.

Amma ‘yarsa mai suna Welwitschia “Tchizé” na son a yi masa jana’iza a killace kuma a binne shi a wani Kabari na musamman a Sifaniya ta yadda ‘ya’yansa za su iya ziyartarsa,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ta ce wasu daga cikin ‘yan uwanta na goyon bayan Kudirin nata, wadanda ke fuskantar zargin cin hanci kuma za a iya kama su da zarar sun saka Kafa a Angola.

Daya daga cikin ‘ya’yan Dos Santos ya ce ba Kasar ce ke da alhakin daukar nauyin jana’izarsa ba kuma iyalinsa ne ya kamata su yanke hukunci.

Maganar cewa ko Kasa na da iko kan gawar shugabanta ba sabon abu ba ne.
An samu irin wannan lamari a Zimbabwe a 2019, lokacin da Robert Mugabe ya rasu shekara kusan biyu da suka wuce bayan ya shekara 37 a kan mulki – inda shugaba mai-ci Emmerson Mnangagwa ya kawo Karshen mulkin nasa tare da goyon bayan sojoji.

Kowa ya yi tunanin za a binne shi ne a Filin Gwaraza na Kasa ( Heroes’ Acre) da ke Birnin Harare.

Ko ma dai mene ne, shi ne ya gina Heroes’ Acre kuma ya binne da yawa daga cikin abokan gwagwarmayarsa, ciki har da Sally matarsa ta farko.

Mista Mnangagwa ya fara gina Kabari na musamman don binne jagoran neman ‘yancin, amma kuma iyalansa ba su amince da hakan ba ganin yadda aka kore shi daga mulki kuma abokan gwagwarmyarsa suka yaudare shi.

Bayan shafe makonni ana taKaddama, iyalinsa sun yi nasara kuma an binne Mista Mugabe, jagora kuma gwarzo a Zimbabwe, a Kauyensu ba tare da wani wakilin gwamnati ba.

Hatta Kenneth Kaunda – shugaban Kasa na farko bayan ‘yancin kai a Kasar Zambia kuma daya daga cikin ‘yan gwagwarmayar neman ‘yanci – bai iya samun wurin da za a binne shi ba ba tare da rikici ba.

A cewar iyalinsa, ya so a binne shi kusa da matarsa ba inda gwamnati ta tanada ba.

Zuwa yanzu dai iyalin nasa ba su yi wata jayayya ba yayin da “KK” – kamar yadda ake kiran sa da shi – na ci gaba da kwanciya a Embassy Memorial Park da ke Lusaka baban birnin Kasar.

Daga gudun hijira zuwa girmamawa
“Wadannan rikice-rikice kan gawarwaki ba sabbin abubuwa ba ne. A nan Ghana, mun saba da irin wannan.

Shugaban Kasarmu na farko Kwame Nkrumah ya rasu a Bucharest na Romania lokacin da yake jinya.
Da farko an binne shi a Conakry, Guinea bayan ya shafe lokaci yana gudun hijira a can. Daga baya aka mayar da gawarsa Ghana. An yi masa jana’izar gwamnati a Accra sannan aka binne shi a Kauyensu na Nkroful.

A lokuta daban-daban za ka dinga jin iyalansa na cewa a dawo musu da gawarsa.

A 2012, shugaban Kasarmu John Atta-Mills ya rasu yana kan mulki amma samun wurin da za a binne shi ya zama aiki.

Wasu daga cikin iyalansa sun nemi a kai gawarsa Kauyensu, sai dai ba su samu wani goyon baya ba a lokacin.

An Kyale wurin da gwamnati ta haKa a matsayin Kabarinsa saboda bai dace da shi ba. Daga baya aka mayar da shi wani wuri daban.

An tsara cewa wurin shaKatawar da aka binne shi ya zama maKabartar shugabannin Kasa.

Tun daga wannan lokaci, wani shugaban Kasar – Jerry Rwlings – yara su.
Ba kai shi wurin da aka binne Shugaba Atta-Mills kawai ba, iyalansa sun zargi gwamnati da aiwatar da hakan ba tare da izininsa ba.

An binne shi a maKabartar sojoji da ke Accra tare da yi masa jana’izar girmamawa.
‘Yan makonni da suka wuce muka yi bikin cika shekara 10 da mutuwar Atta-Mills.
Har yanzu ana cecekuce a kan kushewarsa: wane ne zai kula da ita kuma me za a rubuta a kanta.

Akwai kuma wasu daga iyalansa da ke son a tono gawarsa daga inda gwamnati ta binne shi a Accra zuwa Kuyensu don a sake binne shi.

Saboda haka ina ganin daya daga cikin matsalolin zama shugaban Kasa a Afirka ita ce ba lallai a samu wurin da za a binne mutum ba idan ya rasu,” a cewar ‘yar jaridar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Yadda Za Ka Fara Sana’ar Sayar Da Data

Yadda Za Ka Fara Sana'ar Sayar Da Data

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.