• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Rarara Da Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano: A Ina Gizo Ke Sakar?

by Rabilu Sanusi Bena and Abubakar Sulaiman
6 months ago
in Nishadi
0
Takaddamar Rarara Da Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano: A Ina Gizo Ke Sakar?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta bayyana cewar ta maka mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara a wata kotun majistare da ke Nomansland a birnin Kano inda ta ke tuhumarsa da karya dokar hukumar ta hanyar fitar da wata wakarsa ba tare da ya gabatar da ita gaban hukumar domin tacewa ba.

 

A wata sanarwa da jami’in yada labarai na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya aika wa manema labarai ya ce hukumar tace fina-finai ta aikawa da mawakin sakon korafi dangane da sabuwar wakar da ya saki ba tare da ya kawo an tace ba sai dai mawakin bai bata amsa dangane da korafin data aika mashi ba wanda hakan ne dalilin da yasa hukumar ta garzaya gaban kotun domin kowa zaman doka yake a cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar.

  • Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance
  • Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron G20 A Kasar Brazil

Wakilin hukumar a kotu ya tabbatar da cewa tuni kotun ta aika wa mawakin takardar gayyatar sammaci sai dai ba’a ga fuskarsa ba a ranar 13 ga watan nuwamba a yayin zaman kotun ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Tun kafin wannan lokacin bayan sakin sabuwar wakar hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano ta turawa mawakin sakon neman ba’asi ta hanyar sakon kar-ta-kwana sai dai har kawo wannan lokaci mawakin bai maidowa da hukumar amsar sakon ba.

 

Kamar yadda kowa ya sani ne tace fina-finai, rubuce-rubuce tare da waka na daya daga cikin manyan ayyukan da suka rataya a kan hukumar domin tabbatar da tsafta tare da dora komai a bisa doron doka da oda inji shi.

 

Daya daga cikin makusantan Dauda Kahutu Rarara Abdullahi Al Hikma da ya ke mayar da martani a kan ikirarin da hukumar Tace Fina-finai da dab’i ta jihar Kano ta yi, ya ce ko alama maigidan na sa bai san da wannan umarni da kotu ta bayar ba domin kuwa har yanzu babu wata takarda ta kotu da ta shiga hannun mawakin.

 

Al-hikma ya ce wannan takarda da muka ga tana yawo a kafafen sadarwa wacce wata hukuma a Jihar Kano ta maka mawaki Dauda Kahutu Rarara a kotu, ba a hukumance aka gabatar da ita ba,kuma mun san idan ana karar mutum to za a kai takarda ta sammaci a gidan sa ko wani waje da za a same shi.

 

Amma ba a yi ko daya daga cikin wadannan biyu ba sai dai kawai muka ji wai an kai Rarara kotu,kuma a sanarwar da aka bayar a soshiyal midiya,mu ba mu ga an ce ga kotun da ake neman mu ba kokuma ga ma wakar da aka yi inji shi.

 

Ya kara da cewar na ji wani da yake magana da yawun hukumar Tace Fina Finai ma ya kasa fadar sunan wacce waka ce,kuma mun yi wakoki da yawa a wannan wata wadanda aka sake su saboda haka idan har da gaske yake ya kamata ya fito ya bayyana wacce waka ce.

 

Kuma mu masu bin doka da oda ne munsan cewar babu wanda ya fi karfin kotu saboda haka zamu mutunta umarnin kotu idan muka samu wannan takardar sammacin,ko shugaban kasa ne aka ce an kai shi kotu, to dole zai san wacce kotu aka kai shi, kuma a kan wanne laifi ake neman sa.

 

To kuma mu ma ‘yan kasa ne masu biyayya ga dokokin kasa saboda haka mu ba ma raina kotu, kuma ba ma raina hukuma amma dai wannan takarda ta wannan sammaci da ake fada a kafar sadarwa muka ji ta inji Al Hikma.

 

Da yake amsa tambaya akan ko Rarara ya cigaba da yin wakoki a jahar Kano Al Hikma ya amsa da cewar,yanzu shi Dauda Kahutu Rarara ba wai yana yin wakokin sa a nan Jihar Kano ba ne,ko kuma yana yin wakokin sa a kan iya Jihar Kano,hasali ma wakokin a Abuja ake yin su.

 

Duk lokacin da ka ga ya zo Kano, to wani uzuri ne ya kawo shi, kuma zai yi ya gama kwana daya biyu ya fita,don haka yanzu ya bar Kano ya koma Abuja,to saboda haka ba mu san a ina aka kai wannan takarda ba, kuma har yanzu ba ta riske mu ba inda ta riske mu to za mu yi wa doka biyayya,sai mu sa lauyoyin mu su je su ji ba’asi na abin da ake tuhumar mu da shi, tunda dukkan mu a karkashin doka muke kuma babu wanda ya fi karfin doka.

 

A nata bangaren, hukumar ta yi martani kan ikirarin Rarara inda kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fada a sanarwar da ya fitar cewa, tun a ranar 8/11/2024 kotun mai lamba 47 da ke unguwar Noman’sland a Jihar Kano ta aika wa da mawakin takardar sammaci a ofishin sa da ke kan titin gidan Zoo a Kano.

 

Kuma bayan rashin samun sa kotun ta kara tura masa da sakon kar-ta-kwana ta hanyar tedt message da manhajar WhatsApp indaaka bukaci ya bayyana a gaban kotun a ranar 13/11/2024, dangane da maganar da wakilin mawakin ya yi na cewa ba a Kano mawakin ya yi wakar ba hakan ya tabbatar da cewa mawakin ya kwana da sanin laifin da hukumar take zargin ya aikata inji Sani Suleiman.

 

Haka kuma yana da kyau al’umma su kara fahimtar cewa matsawar dan fim, marubuci ko mawaki ya taba yin rijista da hukumar to dole ne ya bi dokokin hukumar a duk inda yake kamar yadda ya dauki alkawari a yayin da zai cike fom.

 

Daga karshe kakakin ya ce hukumar na da hurumi na saka ido, bayar da shawara ko hukunta duk wani aiki da ya shafi ayyukan da suka rataya a kan ta matsawar ya shigo Jihar Kano ko a ina aka yi aikin,ba lallai sai wanda akayi a cikin jihar Kano kawai ba Suleiman ya tabbatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gimbiyoyin KannywoodTasirin mawaki Rarara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Habaka Tsarin Sadarwa Na 5G Zuwa 5G-A

Next Post

Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

Related

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 days ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 days ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

2 weeks ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

3 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

3 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

3 weeks ago
Next Post
Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

Ra'ayin Matasa Kan Kungiyar 'Yan Ta'adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.