ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Rarara Da Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano: A Ina Gizo Ke Sakar?

by Rabilu Sanusi Bena and Abubakar Sulaiman
2 years ago
Rarara

Kwanakin baya hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta bayyana cewar ta maka mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara a wata kotun majistare da ke Nomansland a birnin Kano inda ta ke tuhumarsa da karya dokar hukumar ta hanyar fitar da wata wakarsa ba tare da ya gabatar da ita gaban hukumar domin tacewa ba.

 

A wata sanarwa da jami’in yada labarai na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya aika wa manema labarai ya ce hukumar tace fina-finai ta aikawa da mawakin sakon korafi dangane da sabuwar wakar da ya saki ba tare da ya kawo an tace ba sai dai mawakin bai bata amsa dangane da korafin data aika mashi ba wanda hakan ne dalilin da yasa hukumar ta garzaya gaban kotun domin kowa zaman doka yake a cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar.

ADVERTISEMENT
  • Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance
  • Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron G20 A Kasar Brazil

Wakilin hukumar a kotu ya tabbatar da cewa tuni kotun ta aika wa mawakin takardar gayyatar sammaci sai dai ba’a ga fuskarsa ba a ranar 13 ga watan nuwamba a yayin zaman kotun ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Tun kafin wannan lokacin bayan sakin sabuwar wakar hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano ta turawa mawakin sakon neman ba’asi ta hanyar sakon kar-ta-kwana sai dai har kawo wannan lokaci mawakin bai maidowa da hukumar amsar sakon ba.

 

Kamar yadda kowa ya sani ne tace fina-finai, rubuce-rubuce tare da waka na daya daga cikin manyan ayyukan da suka rataya a kan hukumar domin tabbatar da tsafta tare da dora komai a bisa doron doka da oda inji shi.

 

Daya daga cikin makusantan Dauda Kahutu Rarara Abdullahi Al Hikma da ya ke mayar da martani a kan ikirarin da hukumar Tace Fina-finai da dab’i ta jihar Kano ta yi, ya ce ko alama maigidan na sa bai san da wannan umarni da kotu ta bayar ba domin kuwa har yanzu babu wata takarda ta kotu da ta shiga hannun mawakin.

 

Al-hikma ya ce wannan takarda da muka ga tana yawo a kafafen sadarwa wacce wata hukuma a Jihar Kano ta maka mawaki Dauda Kahutu Rarara a kotu, ba a hukumance aka gabatar da ita ba,kuma mun san idan ana karar mutum to za a kai takarda ta sammaci a gidan sa ko wani waje da za a same shi.

 

Amma ba a yi ko daya daga cikin wadannan biyu ba sai dai kawai muka ji wai an kai Rarara kotu,kuma a sanarwar da aka bayar a soshiyal midiya,mu ba mu ga an ce ga kotun da ake neman mu ba kokuma ga ma wakar da aka yi inji shi.

 

Ya kara da cewar na ji wani da yake magana da yawun hukumar Tace Fina Finai ma ya kasa fadar sunan wacce waka ce,kuma mun yi wakoki da yawa a wannan wata wadanda aka sake su saboda haka idan har da gaske yake ya kamata ya fito ya bayyana wacce waka ce.

 

Kuma mu masu bin doka da oda ne munsan cewar babu wanda ya fi karfin kotu saboda haka zamu mutunta umarnin kotu idan muka samu wannan takardar sammacin,ko shugaban kasa ne aka ce an kai shi kotu, to dole zai san wacce kotu aka kai shi, kuma a kan wanne laifi ake neman sa.

 

To kuma mu ma ‘yan kasa ne masu biyayya ga dokokin kasa saboda haka mu ba ma raina kotu, kuma ba ma raina hukuma amma dai wannan takarda ta wannan sammaci da ake fada a kafar sadarwa muka ji ta inji Al Hikma.

 

Da yake amsa tambaya akan ko Rarara ya cigaba da yin wakoki a jahar Kano Al Hikma ya amsa da cewar,yanzu shi Dauda Kahutu Rarara ba wai yana yin wakokin sa a nan Jihar Kano ba ne,ko kuma yana yin wakokin sa a kan iya Jihar Kano,hasali ma wakokin a Abuja ake yin su.

 

Duk lokacin da ka ga ya zo Kano, to wani uzuri ne ya kawo shi, kuma zai yi ya gama kwana daya biyu ya fita,don haka yanzu ya bar Kano ya koma Abuja,to saboda haka ba mu san a ina aka kai wannan takarda ba, kuma har yanzu ba ta riske mu ba inda ta riske mu to za mu yi wa doka biyayya,sai mu sa lauyoyin mu su je su ji ba’asi na abin da ake tuhumar mu da shi, tunda dukkan mu a karkashin doka muke kuma babu wanda ya fi karfin doka.

 

A nata bangaren, hukumar ta yi martani kan ikirarin Rarara inda kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fada a sanarwar da ya fitar cewa, tun a ranar 8/11/2024 kotun mai lamba 47 da ke unguwar Noman’sland a Jihar Kano ta aika wa da mawakin takardar sammaci a ofishin sa da ke kan titin gidan Zoo a Kano.

 

Kuma bayan rashin samun sa kotun ta kara tura masa da sakon kar-ta-kwana ta hanyar tedt message da manhajar WhatsApp indaaka bukaci ya bayyana a gaban kotun a ranar 13/11/2024, dangane da maganar da wakilin mawakin ya yi na cewa ba a Kano mawakin ya yi wakar ba hakan ya tabbatar da cewa mawakin ya kwana da sanin laifin da hukumar take zargin ya aikata inji Sani Suleiman.

 

Haka kuma yana da kyau al’umma su kara fahimtar cewa matsawar dan fim, marubuci ko mawaki ya taba yin rijista da hukumar to dole ne ya bi dokokin hukumar a duk inda yake kamar yadda ya dauki alkawari a yayin da zai cike fom.

 

Daga karshe kakakin ya ce hukumar na da hurumi na saka ido, bayar da shawara ko hukunta duk wani aiki da ya shafi ayyukan da suka rataya a kan ta matsawar ya shigo Jihar Kano ko a ina aka yi aikin,ba lallai sai wanda akayi a cikin jihar Kano kawai ba Suleiman ya tabbatar.

Rarara
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Barcelona Ta Kammala Daukar Anthony Gordon Daga Newcastle
Rarara
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

Ra'ayin Matasa Kan Kungiyar 'Yan Ta'adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.