• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Bayani Kan Dashen Dogon-yaro Da Lokacin Amfaninsa

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Takaitaccen Bayani Kan Dashen Dogon-yaro Da Lokacin Amfaninsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Bishiyar Dogon-yaro na fara fitar da ‘ya’ya ne daga shekaru uku zuwa biyar, inda kuma ta ke kammala girma a cikin tsawon shekaru goma.

A duk shekara bishiyar na samar da ya’ya’ da yawansu ya kai kimanin kilogiram 50, haka zalika; bishiyar na shafe dimbin shekaru a duniya ba tare da komai ya same ta ba.

  • Sin Na Goyon Bayan Yunkurin IAEA Na Tabbatar Da Tsaron Tashar Nukiliya Ta Zaporizhzhia
  • Ana Gudanar Da Horo Kan Gina “Koren Babbar Ganuwa” A Afirka A Beijing

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Irin Dogon-yaro Ke Kammala Girma?

Irin Dogon-yaro na da gajeriyar rayuwa; ba ya yin tsawon kwana, domin kuwa yana kai wa daga kwana 10 ne zuwa 12 a lokacin da yake a danyensa. Don haka, ana so ka tabbatar da ka samu ingantaccen Irin da zai yi saurin nuna bayan shuka shi.

Haka zalika, ana so a tabbatar an rufe shi a cikin Tukunya; domin ya kasance ya na samu lema, wanda hakan kan taimaka masa daukar tsawon kwanaki ko mako uku, bayan shuka shi.

Wacce  Kasa Ce Aka Fi Samun Bishiyar Dogon Yaro?

A bisa rahotannin masana a kan harkokin kimiyya da fasaha da kuma binciken da cibiyar bunkasa aikin noma ta kasa da kasa suka gudanar a shekarar 1992 sun bayyana cewa, an fi shuka bishiyar Dogon-yaro a bangaren Asiya da Nahiyar Afirka da kuma wasu kasahe na fadin duniya.

Har wa yau, kusan kashi 60 cikin 100 na al’ummar da ke Kasar Indiya; na shuka wannan bishiya ta Dogon-yaro.

Wace Irin Kasar Noma Bishiyar Dogon-yaro Ta Fi Bukata?

Bishiyar Dogon-yaro ta fi bukatar kasar noma mai inganci, sannan kuma ba a so a shuka Irin a wajen da ruwa ya ke yawan zama.

Wane Bangare Na Bishiyar Dogon-yaro Ne Ake Amfai Da Shi Wajen Sarrafa Magunguna?

Baya ga ita bishiyar ta Dogon-yaro, ana kuma amfani da ganyenta da Irinta da kuma jikinta wajen sarrafa magungunan gargajiya.

Yaya Ake Adana Ganyen Bishiyar Dogon-yaro Ya Dauki Tsawon Lokaci?

Da farko dai, za ka ciro wannan ganye daga jikin wannan bishiya ta Dogon-yaro.

Sannan, matali na biyu kuma ana so ka zuba ganyen a cikin kwano, sai ka rufe shi domin ya tsotse Lemar da ke jikinsa; sannan kuma sai ka rufe shi.

Mataki na uku kuma shi ne, saka shi a cikin firji ko na’ura mai sanyi.

Yadda Ake Tatsar Man Dogon-yaro Daga Ganyensa

Ana bukatar a nika shi, sannan sai a dora shi a kan wuta a tafasa shi ya dauki kamar minti 15, bayan ka sauke shi daga wutar sai ka bar shi ya yi kamar awa biyu ko sama da haka.

Daga nan, sai ka adana shi a wurin da yake a bushe; kana kuma ka tabbatar da cewa, rana ba ta kai ga inda yake ba.

Ana Samun Dimbin Kudaden Shiga A Noman Bishiyar Dogon-yaro

A yanzu haka, bishiyar Dogon-yaro na kara samun karbuwa a fadin duniya, musamman ganin yadda fannin ke samar da kudaden shiga masu daman gaske, haka nan kuma akwai masa’antu da ke sayen sa; domin sarrfaa shi zuwa wasu nau’ikan abubuwa da dama kamar: magunguna, man shafawa da sauran makamantansu.

Har ila yau, bishiyar Dogon-yaro na jurewa fari; sannan kuma bishiyar ta fi son yanayin da bai wuce 21°C zuwa 32°C ko kuma  70°F ko 90°F.

Bugu da kari, wani kwararre a fannin wannan noma na bishiyar Dogon-yaro, Dakta Abdullahi Ahmed Yar’adua ya bayyana cewa,  lokaci ya yi da gwamnatin tarayya za ta mayar da hankali wajen bunkasa noman Dogon-yaro fiye da yadda Kasar Indiya ke yi a halin yanzu.

Dr Yar’adua ya tabbatar da cewa, Indiya na da kimanin bishiyar Dogon-yaro da suka kai kimanin miliyan 20, inda ya kara da cewa; daga shekarar 1985 zuwa  1995, gwamnatin kasar na samun kudaden shiga da suka tasamma kimanin dala biliyan 2.5 daga man da take samu daga wannan bishiya ta Dogon-yaro.

Sannan ya sanar da cewa, ana sarrafa ganyen wannan bishiya wajen sarrafa takin zamani, inda ya dora laifin yadda fanin ke samun koma baya a kan yadda shugabanin kasar nan ko kadan ba sa mayar da hankali kan noman Dogon-yaro.

Haka zalika, ya kuma koka a kan yadda aka yi watsi da masa’antar noman Dogon-yaro, wadda tsohuwar gwamnatin Cif Olusegun Obasanjo ya kafa a Jihar Katsina.

Dr Yar’adua ya kuma shawarci gwamnati ta mayar da hankali wajen noman bishiyar Dogon-yaro, musamman ganin yadda ake samun kudaden shiga masu masu dimbin yawa a sauran kasashen duniya daban-daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Kaduna: Rikicin Bashi Da Rashin Sanin Tsarin Gudanar Da Mulki

Next Post

An Damke Wasu ‘Yan Nijeriya Kan Zargin Tilasta Wa Dan Australiya Tura Masu Hotuna

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

2 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

2 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

3 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

1 week ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

1 week ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
An Damke Wasu ‘Yan Nijeriya Kan Zargin Tilasta Wa Dan Australiya Tura Masu Hotuna

An Damke Wasu ‘Yan Nijeriya Kan Zargin Tilasta Wa Dan Australiya Tura Masu Hotuna

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.