• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Nazari Kan Rayuwar Sadiya Umar Faruk

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Adon Gari
0
Takaitaccen Nazari Kan Rayuwar Sadiya Umar Faruk
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sadiya Umar Faruk ‘yar siyasa ce a Nijeriya, ta taba rike mukamin Ministan Kula da Jin Kai da Kula da Bala’o’i da Ci Gaban Al’umma.

Shugaba Muhammadu Buhari ne ya nada ta a watan Yulin 2019. Sadiya Umar Faruk ta kasance minista mafi karancin shekaru a majalisar ministocin tarayya wadda ta shude. Ta yi aiki a matsayin kwamishiniyar Tarayya ta Hukumar ‘Yan Gudun Hijira, baki da mutanan cikin gida (NCFRMI) daga Oktoban 2016 zuwa Agustan 2019.

  • GORON SALLAH
  • Hajjin Bana: Sheikh Muhajjadina Ya Nemi Hukumar Alhazai Ta Kara Kaimi

Aikinta da shugaba Muhammadu Buhari ya samo asali ne tun zamanin da Buhari na matsayin shugaba kuma dan takarar shugaban kasa na rusasshiyar jam’iyyar ‘Congress For Progressibe Change,’ (CPC) lokacin da Sadiya ta kasance ma’ajin jam’iyyar CPC ta kasa sannan kuma ma’ajin jam’iyyar All progressibes Congress APC.

Sadiya Umar Faruk ta samu nasarori da dama tun lokacin da aka kafa ma’aikatar jin kai da kula da bala’o’i a watan Agustan shekarar 2019, ya zuwa yanzu akalla ‘yan Nijeriya miliyan 20 ne aka bai wa tallafi ta hanyar tsare-tsare na zamantakewar al’umma daban- daban da tsare-tsare na ma’aikatar.

Haka nan kuma an bayyana cewa, a karkashin shirin ciyar da makarantu na gidauniyar, jimillar yara miliyan 9.9 daga firamare 1 zuwa 3 a makarantun gwamnati a duk fadin kasar, ana ciyar da abinci mai zafi a duk rana, inda dalibai 126,000 ke cin gajiyar girkin.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

A zamaninta ta inganta wa ma’aikatar ta samu damar sama wa matasa kusan 1,664,774 da shirya- shiryen da suka kammala karatu da wadanda ba su kammala karatu ba a karkashin shirin N-power.

A farkon watan Yulin 2022 Sadiya Umar Faruk ta ba da sanarwar bayar da tallafin tsabar kudi ga marasa galihu a Oshogbo, Jihar Osun.

A matsayinta na mai girma minista tana ba da jagoranci a cikin ci gaban manufofin jin kai da ingantaccan hadin kai na ayyukan agaji na kasa da kasa: tabbatar da dabarun magance bala’i, shirye-shirye da amsawa da gudanar da tsarawa da aiwatar da shirye-shiryen hadaddun jama’a da tsare-tsare na adalci a cikin Nijeriya dai dai da ma’aikatar.

Kafin nada ta a matsayin minista Sadiya Umar Faruk tana da tarihi a matsayin mai girma Kwamishiniyar Tarayya Ta Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijira Da Bakin Haure (NCFRMI).

Ta fito da wani Sabin taswirar dabarun aiki don sake mayar da hukumar don daukar nauyin jagoranci a matsayin kungiyar jin kai ta Nijeriya da kuma kawo ayyukan hukumar zuwa matsayi a duniya.

Sabuwar taswirar dabarun hukumar ta mayar da hankali ne kan samar da mafita mai dorewa ga wanda abin ya shafa tare da jaddada kayyadaddun hanyoyin yin amfani da bincike, tattara bayanai da tsare-tsare don sake saitawa, gyarawa, sake hadawa, da sake dawo da duk mutunen da suka cika a cikin hukumar.

Ofishinta yana aiki hannu da hannu da hukumar kula da nakasassu ta kasa, karkashin jagorancin mista James Lalu, don tabbatar da hada nakasassu fiye da miliyan 30 a cikin al’amura da suka shafi kasa da jama’arta. Don haka ta kaddamar da cibiyar samar da takaddun Lantarki na Nakasassu da ke cibiyar masu nakasa da ke Abuja.

Sadiya Umar Faruk an haife ta 5 Nuwamba 1974, shekarunta sun kasance 48 kenan, ‘yar garin Zurmi ce dake Jihar Zamfara.

Sadiya Umar Faruk ta auri shugaban hafsan sojan sama tana matsayin minista a watan satumba 24 shekara ta 2020.

Sadiya Umar Faruk ta yi fatali da jita-jita ko kuma labaran karya  game da auren shugaba Buhari.

Ministan agaji da agajin gaggawa da masifu da cigaban jama’a Sadiya Umar Faruk ta mika ayyukan ma’aikatar ga babbab sakataren dindindin Dakta Nasir Sani Gwarzo mni. NPOM, bayan shekaru uku da rabi da ta yi tana kyakkyawar hidima ga bil’adama da kuma karshen zamanta a matsayin ministar majagaba.

Sadiya Umar Faruk ta mika takardun da ke kunshe a cikin litattafai guda biyu, na aikinta a ma’aikatar, a karshen taron jin kai na Nijeriya karo na daya da ma’aikatar ta shirya a ranar juma’a a Abuja.

A nata jawabin, ministar ta godewa babban sakatare, daraktoci, ma’aikatan ma’aikatar da kuma Ofishinta bisa dimbin tallafin da aka ba ta a tsawon lokacin da take rike da mukamin.

Sadiya Umar Faruk ta bukaci ma’aikatan da su jajirce wajan ganin sun cimma burin shugaban kasa Muhammadu Buhari na fitar da masu karamin karfi daga kangin talauci.

Na mika wadannan takardun aikin a hukumance a matsayina na majagaba a ma’aikatar jin kai da ci gaban bala’o’i da ci gaban al’umma a cikin shekaru uku da rabi da suka gabata.

Na gode kwarai da goyon bayanku ya yin da ta mika wa babban Sakatare, Dakta Nasir Sani- Gwarzo.

Da ya ke mayar da martani, Sakataran dindindin ya godewa ministar tare da yi mata fatan alheri a ayyukanta na gaba.

Ministan ta ce ma’aikatar ta ta ta samu damar kara wa rayuwar marasa galihu da iyalansu kima a cikin shekaru hudun da suka gabata kuma da kara yin wani abu da za ta iya kai wa ga gidaje da dama a Nijeriya amma ta yaba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan yadda ya ke da hangen nesansa wajen samar da sabuwar hidima.

Ministan ta sanar da cewa a cikin tsawon lokacin da ake bitar ma’aikatar ta samu damar tsarawa da aiwatar da shirin ciyar da abinci na gida-gida na kasa, wanda a kullum ke samar da abinci mai gina jiki ga dalibai 9,990,862 a jihohi 36 da babban birnin tarayya Abuja tare da samar da ayyukan yi ga kasa da kasa.

A lokaci guda kuma Sadiya ta ce a kalla mutane 1,940,325 marasa galihu da aka zabo daga dukkan sassan Nijeriya suna samun tallafin kudi na Naira 5000 duk wata a karkashin shirin ma’aikatar da ke ba da tallafin kudi na musamman, wanda kuma ke samun tallafin Bankin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SadiyaTarihitsohuwar Minista
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Amurka Na Da Bukatar Karfafa Hadin Gwiwa, In Ji Firaministan Kasar Sin

Next Post

Firaministan Kasar Mongoliya Ya Yabawa Ra’ayin Kasar Sin Na Zaman Jituwa Da Amincewa Da Bambanci

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

5 days ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

3 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Adon Gari

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

6 months ago
Next Post
Firaministan Kasar Mongoliya Ya Yabawa Ra’ayin Kasar Sin Na Zaman Jituwa Da Amincewa Da Bambanci

Firaministan Kasar Mongoliya Ya Yabawa Ra’ayin Kasar Sin Na Zaman Jituwa Da Amincewa Da Bambanci

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.