ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ya Karu A Nijeriya Da Kashi 14 Cikin 100

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Talauci

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar da wata kididdiga da ta nuna talauci ya karu a Nijeriya da kashi 14 a cikin 100.

Ta bayyana cewa farashin kayayyakin da ake amfani da su tare da nuna cewa an sami hauhawan farashi da kashi 17.81 a watan Mayu idan aka kwatanta da watan Afrilu da aka sami kashi 16.82 a wannan shekarar duk da yake ya ragu ne a kan abun da aka samu a watan Mayun shekarar da ta gabata ta 2021 da aka sami kashi 17.93.

  • Farashin Kalanzir Da Gas Ya Karu Da Kashi 88 A Cikin Shekara Daya – NBS

Talaudci da kuncin rayuwa a cikin kasa na ta karuwa bisa alamu wanda lamarin ba Nijeriya ba ne kawai duk duniya ne. Bankin Duniya daga baya-bayan nan ya haskako karuwar kuncin rayuwa kusan ilahirin kasashen duniya za su fuskanci wannan matsalar.

ADVERTISEMENT

Bankin Duniya ya bayyana cewa habakar tattalin arziki ya yi kasa da kashi 2.9 cikin dari daga kashi 5.7 cikin dari da aka hassaso a shekarar 2022. Shugaban Bankin Duniya, Dabid Malpass ya yi gargadin cewa yakin Ukraine da annobar Korona da ya janyo rufe China waDanda suka janyo tashin farashin abinci da sauran kayayyakin bukatun yau da kullum su suka shafi tattalin arziki.

Idan aka duba kyau za a ga cewa kuncin rayuwa ba Nijeriya ne kadai ba, ko’ina ne a duniya, akwai kasashe sama da 25 a duniya da suke da kuncin rayuwa. Alal misali Turkiyyya tana da kuncin rayuwa da kashi 73.5 cikin 100, a yayin da yaki ya kara kuncin rayuwa a Sudan ya karu da kashi 192.2 cikin 100.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Rasha da Ukraine kuncin rayuwa ya karu da kashi 18 da 17 cikin 100, idan aka dawo nan Afrika kuwa, Ethiopia yana da kuncin rayuwa ya kai kashi 37.7 cikin 100. Ghana da Angola da Sierra Leone sun kai kashi 27.6 da 23.42 da 22.44 cikin 100 na kuncin rayuwa.

A lokacin da yake magana kan ci gaba da kuncin rayuwa, Mataimakin Gwamnan babban Bankin Nijeriya a fannin tsarin tattarin arziki, Kingsley Obiora ya ce tattalin arzikin duniya yana tafiya ne cikin wani mawuyacin hali.

Ya ce, “Mun ga yadda farashin kayayyaki suka yi tashin gwauron zabi musamman abinci da muke amfani da shi, sakamakon rikicin Ukraine da Rasha wadanda suke fitar da kayayyaki.

“Mun ga yadda harkokin kasuwannin duniya ta kasance bayan rufe China da aka yi wanda duk mun san wadannan nan a yanzu su ne suke samar da abubuwa a duniya. Mun ga yadda ake kokarin daidaita bukatuwar abu, kuma wannan dalilin ne ya haifar da tsadar kayayyaki.

“Mun kuma ga yadda aka rasa ayyukan yi a duniya don wasu sun zabi su yi aiki daga gida. Dukkanin wadannan abubuwa su ne suka haifar da kuncin rayuwa a duniya. Za ka iya zuwa Burtaniya da Amurka a baya can babu kuncin rayuwa, amma a yanzu sun shiga ciki.

“A yanzu a Burtaniya suna da kashi 6 cikin 100, a yayin da Turai ake da kashi 9 cikin 100. Idan kuwa aka je Argentina alal misali, suna da kuncin rayuwa sama da kashi 70 cikin 100. Amma idan muka duba a Nijeriya idan muka kwatanta da sauran duniya za mu iya cewa muna da kashi 17 cikin 100 ne kawai.

A lokacin da yake sharhi kan kuncin rayuwar da Nijeriya ke ciki a halin yanzu, kwararren mai sharhin al’amuran yau da kullum a FDTM, Lukman Otunga ya bayyana cewa akwai lokacin da Nijeriya ta yi shiru a kan shiga wani kuncin rayuwa da aka yi.

Ya ce, “A daidai lokacin da wasu kasashe a duniya suke kokarin duba farashin kayayyaki, kasar da ta fi kowacce kasa girman tattalin arziki a Afrika kuma take da masaniyar yadda za ta sassauta kuncin rayuwa. Wannan dabara ce da CBN ya gaza sauya shi wajen inganta tattalin arzikin kasa da habaka shi.

“A yanzu kuncin rayuwa a Nijeriya ya karu sosai a watanni hudu a jere zuwa kashi 17.71 cikin 100 a watan Mayu.

Wanda za a iya cewa shi ne mafi muni tun daga watan Yunin bara, hakan ya sanya aka sami karin farashin abinci da farashin man dizil da kuma karancin dalar Amurka.

Wannan kuma shi ne yadda kayayyaki suke kara tashi a duniya da shirye-shiryen zabe wadanda su ne abubuwan da suke kara tsananin matsalolin da ake fuskanta.

Musamman bayan kalaman da hukumar IMF ta yi game da farashin kayayyaki, inda ta ce zai tashi daga tsakanin kashi 18 da kashi 22 cikin 100 a shekarar 2022.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Nasarori Goma Da BRICS Ta Samu A Bana

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.