• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ka iya kashe a kalla naira biliyan 188.25 a kowace shekara wajen biyan tallafin kudi na wutar lantarki ga asibitocin gwamnati sama da 75 da manyan makarantu su 300 a sassan kasar nan.

Wannan na zuwa ne biyo bayan amincewa da gwamnatin tarayya ta yi da sassaucin kaso 50 cikin 100 na kudin lantarki ga asibitocin gwamnati da kuma manyan makarantu a fadin Nijeriya.

  • Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Jana’izar Mahaifiyar Yar’Adua
  • Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

A watan Afrilu ne hukumar kula da wutar lantarki ta sanar da karin kudin wutar lantarki ga masu amfani da rukunin A na karin kudi da aka samu da kaso 300.

Tun da farko dai, ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya yi alkawarin cewa gwamnatin tarayya za ta tallafa wa asibitoci da manyan makarantun da suke mallakinta wajen rage musu kudin wutar lantarki da suke biya.

Ya ce, gwamnati tana sane da irin kudin da asibitoci da manyan makarantu ke kashe wajen biyan kudin wuta, wanda hakan ya zama musu babban kalubale.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

Karamin ministan lafiya, Dakta Tunji Alausa, ya sanar a ranar Alhamis cewa gwamnatin tarayya ta amince da biyan tallafin lantarki na kaso 50 ga asibitocin gwamnati.

A cewar Alausa, wannan an yi ne domin rage wa asibitocin kashe maguden kudade wajen biyan kudin wuta wanda hakan ke shafar majinyata da ya sanya ake cazansu kudi da yawa.

Binciken da majiyarmu ta gudanar, ya nuna cewa gwamnatin tarayya za ta iya kashe naira miliyan 50 ga kowace asibiti daga cikin sama da 75, inda ya kai kimanin biliyan 3.75 a kowace wata, wato biliyan 45 a shekara guda.

Shugaban kwalejin fasaha ta Yaba da ke Legas, Dakta Ibraheem Abdul, ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa wannan, yana mai cewa tabbas hakan zai taimaka wajen kyautata koyarwa da kuma rage wa makarantu tsula kudi ga dalibai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsibitiBola Ahmed TinubuNepaPower
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Kaddamar Da Sassakar Tunawa Da Gasar Olympics Ta Paris 

Next Post

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

Related

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka
Labarai

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

3 hours ago
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira
Labarai

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

4 hours ago
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
Labarai

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

5 hours ago
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi
Labarai

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

7 hours ago
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

9 hours ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

10 hours ago
Next Post
Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.