• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

A yau Talata 15 ga wata, ma’aikatar tsaron kasar Sin ta bude taron shugabannin matasa irinsa na farko na dandalin tattaunawar zaman lafiya da tsaro na Sin da Afrika, wanda zai gudana har zuwa ranar 19 ga wata.

Manufar taron wanda zai samu halartar manya da matsakaitan hafsoshin soja kusan 90 daga kasashen Afirka fiye da 40, ita ce kara cimma matsaya, da karfafa hadin kai a fannin zaman lafiya da tsaro, da ba da gudummawa ga gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta Sin da Afirka.

  • Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
  • Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Tsaro wani muhimmin ginshiki ne na ci gaba da tabbatar da walwalar al’umma. Kafin al’umma ta samu walwala ko wadata, ko bunkasar tattalin arziki, sai ta samu tsaro da kwanciyar hankali. Haka kuma duk wani arziki da kasa ke tinkaho da shi, to ba za ta iya cin gajiyarsa ba muddin tana fama da matsaloli na tsaro.

Ba makawa koma bayan tattalin arziki da mawuyacin halin da kasashen Afrika ke fama da su na da alaka mai zurfi da tabarbarewar tsaro da yaki ci yaki cinyewa.

Hakika tunanin kasar Sin abu ne mai matukar burgewa domin ta kan mayar da hankali ne ga neman mafita mai dorewa. Kamar yadda muka sani, matasa, su ne kashin bayan ci gaban kowace al’umma, haka kuma su ne masu tafiya da zamani da ganin irin abubuwan dake faruwa a cikin al’umma. Baya ga haka, su ne za su fi fahimtar yadda bata-gari ke tunani.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Gayyato matasan Afrika da Sin ta yi, yana da muhimmanci ga warware matsalar da kasashensu suke fama da su, kasancewarsu na da kaso mai yawa cikin al’umma, kuma akasari su ne suka fi jin radadin tashe-tashen hankula da yake-yake, don haka yin watsi da ra’ayoyinsu, ba zai taba kawo mafita ga halin rashin tsaro ba. Amma sanya matasa cikin manufofi da dabarun tsaro da na raya kasa, zai kai ga warware tushen matsalolin.

Bugu da kari, tunaninsu ya bambanta da na wadanda suka gabace su, don haka za su iya kirkiro sabbin dabarun samar da mafita da za su kore wadanda aka dade ana amfani da su.

Tabbas ba su dama na tattaunawa da Sin ta yi, ya samar da wata mahanga ta daban, wadda muke sa ran za ta taimaka wajen sauya alkiblar yaki da matsalolin tsaro da za su kawo mafita. Bugu da kari, bisa la’akari da zuwansu, za su koyi darrusa daga kasa mai gogewa kamar Sin, wadda duk da yawan al’ummarta, tabbatar da tsaronsu bai taba gagararta ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
Daga Birnin Sin

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
Daga Birnin Sin

An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

October 12, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

LABARAI MASU NASABA

Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

October 12, 2025
An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

October 12, 2025
Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

October 12, 2025
Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

October 12, 2025
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

October 12, 2025
Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

October 12, 2025
Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.