• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron SGI Na Gudana Kan Sauyin Yanayi Karo Na 28

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Taron SGI Na Gudana Kan Sauyin Yanayi Karo Na 28
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taron Saudi Green Initiative (SGI) na gudana karo na 28 da hadin guiwa da Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi (COP28), wanda ya samar da dandalin tattaunawa tsakanin masu ruwa da tsaki da dama don kawo dakile matsalar sauyin yanayi.  

Mai Martaba Mohammed bin Salman bin Abdulaziz Al Saud, yarima mai jiran gado, kuma shugaban kwamitin koli na inganta koren yanayi a Saudiyya ne ya kaddamar da shirin na Saudiyya Green Initiative a shekarar 2021.

  • Nijeriya Ta Sake Bukatar Sojin Nijar Su Saki Bazoum
  • Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan N207.75bn A Matsayin Kasafin 2024

A taron SGI, jami’an Saudiyya sun mayar da hankali kan ci gaban da ake samu kan burin Masarautar na cimma matsaya mai kyau nan da shekarar 2060.

Manufofin taron shi ne samar da yanayi na duniya ta hanyar aiwatar da tsare-tsare sama da 80 na jama’a da na kamfanoni masu zaman kansu da ke wakiltar zuba jarin sama da dalar Amurka biliyan 188, don samar da kyakkyawar makoma ga kowa.

Saudiyya na son cimma burinta na rage hayakin Carbon da tan miliyan 278 a kowace shekara nan da shekarar 2030.

Labarai Masu Nasaba

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a

Masarautar na da nufin yin cimma daidaiton makamashi don samar da wutar lantarki ta hanyar samun iskar gas da makamashi da kusan kashi 50 nan da shekarar 2030.

Sama da tsare-tsare 40 sun riga sun fara aiki, wanda ke tallafawa kai tsaye ga ci gaban da ke na dasa itatuwa miliyan 600 da kuma gyara wasu miliyan takwas nan da shekarar 2030.

A yanzu za a aiwatar da dabarun inganta dazuka da kuma gyara ciyayi da furanni don magance matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da shi a yanzu.

Za a aiwatar da taswirar bishiyoyi biliyan 10 a matakai biyu; kashi na farko (2024-2030), zai mayar da hankali kan yanayin muhalli. Mataki na biyu zai habaka yunkurin samo dabaru.

Yunkurin da Saudiyya ke yi a fadin Masarautar zai taimaka wajen samar da ayyukan yi a bangarori da dama, tare da taimakawa wajen yaki da kwararowar hamada da yashi, da rage tasirin guguwar kura da inganta rayuwa ga mazauna kasar.

A halin yanzu, kashi 18.1 na filaye da 6.49% na muhallin ruwa a Saudiyya suna samun kariya.

Tattaunawar SGI, wacce aka fara a ranar 30 ga watan Nuwamba, za ta ci gaba da gudana har zuwa karshen ranar 12 ga Disamba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SaudiyyaSauyin YanayiSGITaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan N207.75bn A Matsayin Kasafin 2024

Next Post

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

Related

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

17 hours ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a

2 days ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

3 days ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

6 days ago
Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

1 week ago
Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika
Kasashen Ketare

Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika

2 weeks ago
Next Post
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.