• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arziki: Gwamna Lawal Ya Nemi Hadin Gwiwar Masu Zuba Jari Na Kasashen Afirka A Taron AFREXIM A Kenya 

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Tattalin Arziki: Gwamna Lawal Ya Nemi Hadin Gwiwar Masu Zuba Jari Na Kasashen Afirka A Taron AFREXIM A Kenya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na mayar da hankali wajen lalubo hanyoyin haɗin gwiwar ci gaba na gaskiya da adalci da za su amfani zamantakewa da tattalin arzikin jihar.

 

Gwamnan ya wakilci Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma ya kasance babban baƙo a taron ƙara wa juna sani na Haɗin Gwiwa na Ƙasashen Afirka karo na huɗu, wanda aka gudanar ranar Litinin a otel ɗin Swiss Grand Royal da ke garin Kisumu ta ƙasar Kenya.

  • An Kama Dillalin Safarar Makamai Dan Aljeria A Zamfara 
  • Xi Ya Bukaci A Aiwatar Da Kudurin Kwamitin Sulhun MDD Kan Batun Palastinu

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, taron da aka fara daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Nuwamba, Shugaban Ƙasar Kenya, Dr. Williams Ruto ne ya buɗe taron.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

Sanarwar ta ƙara da cewa, taken taron na AfsNET shi ne “Yin amfani da AfCFTA don Samun Ɗorewar Cinikayya da Zuba Jari: Hanyar Ci Gaba ga Ƙasashen Afirka.”

 

Gwamna Lawal, wanda ke gabatar da saƙon fatan alheri a madadin Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, ya ce taken taron na AfsNET na bana ya yi daidai da muradun ci gaban gwamnatocin ƙasashen Afirka. “Taron na ƙalubalantar mu da mu daidaita dabarunmu da albarkatunmu don buɗe damar kawo sauyi a harkar Cinikiyyar Ta Gaskiya d Adalci A Afirka (AfCFTA).

 

“A Nijeriya, mun fahimci muhimmiyar rawar da ƙananan gwamnatocin ƙasashe ke takawa wajen tafiyar da harkokin kasuwanci, zuba jari, da ci gaban tattalin arziki. Jihohinmu 36 cibiyoyi ne na tattalin arziki daban-daban, kowannensu yana da rawar da yake takawa ta musamman da ke ba da gudunmawa ga tattalin arzikin ƙasa.

 

“Ana iya ganin babban misalin hakan a shirin Agro-Allied Industrial Zone ta Jihar Kaduna, shirin haɗin gwiwar gwamnati da ɗaiɗaikun jama’a da aka tsara don inganta noma tare da sarrafa anganin gona don fitarwa zuwa waje.

 

“Wannan aikin yana nuna yadda masu mulki za su iya amfani da albarkatun cikin gida da kuma tsarin AfCFTA don haɓaka ƙimar kasuwanci da faɗaɗa damar kasuwanci a duk faɗin Afirka. Hakazalika, yankin AfCFTA na Lekki ya zama abin koyi na samar da masana’antu da kuma jawo hannun jari kai tsaye daga ƙetare a jihar Legas. ”

 

A wajen taron tattaunawa kan samar da mafita mai ɗorewa ga ci gaban yankin Afirka, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, haɗin gwiwa ne zai kawo daidaito a bangaren ci gaban tattalin arziki.

 

“A matsayina na gwamna a yankin Arewa maso Yamma na Nijeriya, tare da haɗin gwiwar wasu gwamnoni shida, mun ƙirƙiro Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma don bayyanawa tare da daidaita manufofin da za su samar da haɗin kan yankin don samun ci gaba mai ɗorewa. Wannan ya riga ya fara samar da sakamakon mai kyau a yankin.

 

Dangane da batun tsaro, Gwamna Lawal ya jaddada cewa, in ba tare da ingantaccen tsarin muhalli ba, gwamnatoci ba za su iya samar da ayyukan jin daɗin jama’a yadda ya kamata ba kamar ilimi, kiwon lafiya, daidaiton jinsi, kawar da rashin daidaito, da samar da ayyukan dogaro da kai ga maau ƙaramin ƙarfi, waɗanda su ne muhimman abubuwan da ake buƙata don ci gaba mai ɗorewa.

 

“Tsarin mulki ya taƙaita ƙarfin Gwamna ta fuskar samar da tsaro ga al’ummar da yake mulka; duk da haka, mun yi namijin ƙoƙari wajen ganin mun tabbatar da cewa muhallinmu ya kasance cikin kwanciyar hankali ta hanyar kafa Rundunar Kare Al’umma (CPG), wadda ta daƙile matsalar rashin tsaro da ake fuskanta kafin zuwan gwamnatina.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Next Post

Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

3 minutes ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

1 hour ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

3 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

5 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

8 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

15 hours ago
Next Post
Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.