ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

A kwanan baya an gudanar da taron koli na duniya a kan intanet a garin Wuzhen na kasar Sin inda kwararru da masana har ma da manazarta suka taru domin waiwaye adon tafiya kan irin ci gaban da ake samu a bangaren intanet da kuma alkiblar da aka dosa.

 

A yayin gudanar da wannan taro, rahoton da Cibiyar Binciken Harkokin Intanet ta kasar Sin ta fitar na 2024 ya nuna har yanzu kasar Sin tana jan zarenta a matsayi na biyu wajen samun ci gaban intanet a duniya tare da maki 69.00. Bugu da kari, kasar ce a kan gaba wajen gabatar da bukatar neman ikon mallakar sabbin abubuwan da aka kera masu amfani da kirkirarriyar basira ta AI. Hukumar Kula da Ikon Mallakar Kayan Fasaha ta Duniya ta ce kasar ta shigar da bukatun neman hakkin mallaka fiye da 38,000 daga shekarar 2014 zuwa 2023.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030
  • Shehu Mahy Inyass Ya Sanar Da Sauye-sauye A Tafiyar Tijjaniya A Nijeriya

Bayan haka, kasar Sin ta kara himmar bunkasa fasahar sadarwa inda zuwa watan Yunin bana aka samu masu wayoyin salula miliyan 889 dake amfani da fasahar intanet mai karfin 5G da kasar ta kirkiro.

 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Zurfafa bincike da aiwatar da shi da kasar Sin ke ci gaba da yi a fannin kimiyya da fasaha yana haifar da da mai ido. Kasar ta nuna irin ci gaban da take samu a fannin fasahar zamani a yayin da ta yi amfani da tawagar sintiri na tsaro da babu dan Adam ko daya a ciki sai karnukan mutum-mutumi da jiragen ruwa da motoci marasa matuka masu amfani da kirkirarriyar basira, yayin gudanar da taron kolin intanet na duniya a garin Wuzhen.

 

Su wadannan karnuka na mutum-mutumi an sanya musu kaifin basira ta yadda suke iya daidaituwa da wurare mabambanta da kuma ko wane yanayi na aiki. Ko wane kare a cikinsu yana iya tafiyar tsawon mita uku zuwa shida a cikin dakika guda. Sannan ta hanyar kyamarar da aka makala masa yana iya tattara bayanan bidiyo na duk inda aka tura shi tare da aikawa a kan lokaci zuwa cibiyar karba da bayar da umarni. Hikimar hakan ita ce daukar mataki nan take da yin gargadi a kan duk wata barazana da ka iya tasowa.

 

Har ila yau kasar Sin ta kera wannan kare na mutum-mutumi ne ta yadda za a iya amfani da shi ta fuskar gudanar da aikace-aikace mabambanta. Hakan ya sa aka sanya masa lasifika don isar da sako ga wurin da aka tura shi, da na’urar kararrawa mai abin latsawa guda daya don ankararwa, da akwatin kiwon lafiya na wucin-gadi domin taimaka wa bayar da taimakon gaggawa, da sauran wasu ayyuka da suka shafi motsi da hannu da taka muhimmiyar rawa wajen yada labarai da kuma aikin ceto.

 

Haka nan, da yake garin da ya karbi bakuncin taron yana kunshe ne da manyan hanyoyin ruwa, an yi amfani da jiragen ruwa marasa matuka na zamani da kasar Sin ta kera wadanda suka yi aikace-aikace cikin sarrafa kansu bisa amfani da fasahar sadarwa ta 5G wacce ta taimaka wajen nuna bayanan ayyukan sa-ido da kuma gwajin yanayin ruwa a kan lokaci. Duk dai a tawagar ta sintiri, an yi amfani da motoci marasa matuka domin tabbatar da tsaro ta hanyar fasahar zamani.

 

Tabbas, bisa yadda kasar Sin ke yaye injiniyoyi sabbin jini sama da miliyan 4 a kowace shekara da kuma makudan kudin da take zubawa don zurfafa binciken kimiyya, za a ci gaba da ganin nasarorinta a bangaren fasaha mai matukar alfanu ga rayuwar dan Adam a duniya baki daya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Sin Ta Kafa Dakin Samar Da Kayan Al’adun Gargajiya Fiye Da 9100

Sin Ta Kafa Dakin Samar Da Kayan Al’adun Gargajiya Fiye Da 9100

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.