• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Yana Farfaɗowa Sannu A Hankali – Tinubu 

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Tattalin Arzikin Nijeriya Yana Farfaɗowa Sannu A Hankali – Tinubu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa, sannu a hankali tattalin arzikin Nijeriya na farfaɗowa, yana mai alaƙanta cigaban da aka samu da sauye-sauyen da gwamnatin sa ke aiwatarwa a sassa daban-daban.

 

Shugaban ya bayyana haka ne a garin Yenagoa na Jihar Bayelsa a ranar Alhamis a jawabin sa na buɗe babban taron shekara na Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE).

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje
  • An Kama Wasu Ƴansanda Kan Zargin Kisan Ɗalibin Jami’ar Kwara

Da yake magana ta bakin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, Shugaba Tinubu ya ce ya shafe watanni goma sha takwas da suka gabata yana kafa harsashin samar da Nijeriya mai arziki.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Ya ce: “Ina farin cikin sanar da ku cewa ta hanyar gyare-gyaren mu, muna ganin tattalin arzikin mu yana farfaɗowa. A yau, biyan ɗin bashin da muke yi da kuɗin shiga ya sauko sosai daga kusan kashi 100 zuwa kusan kashi 65.

 

“An shafe watanni goma sha takwas da suka gabata wajen aza harsashin wannan kyakkyawar manufa ta samar da cigaban Nijeriya.

 

“Wannan shi ne abin da Ajandar Sabunta Fata ke tattare da shi – wato sake farfaɗo da imani da fatan dukkan ‘yan Nijeriya kan yadda ƙasar su za ta bunƙasa da kuma samar da yanayin da zai bai wa kowa da kowa a cikin ta damar bunƙasa.

 

“Amma mun fahimci cewa akwai wasu manyan cikas da ke kan hanyar fito da ɗimbin abubuwan da Nijeriya ke da su. Kuma mun yi amfani da lokaci da kuzari kuma mun mai da hankali wajen magance waɗannan.

 

“Biyu daga cikin manyan abubuwan da suka fi muhimmanci sanannu ne a gare ku: tsarin tallafin man fetur wanda ya hana mu samun biliyoyin daloli a duk shekara da za a iya saka hannun jari da su a muhimman abubuwan more rayuwa, da tsarin musayar kuɗaɗen ƙasashen waje wanda za a iya amfani da shi ta hanyar da ba ta dace ba.”

 

Ya bayyana cewa sakamakon gyare-gyaren da aka yi, kuɗaɗen shiga na dukkan matakai uku na gwamnati – wato Tarayya, Jihohi, da Ƙananan Hukumomi – ya samu bunƙasa sosai, wanda hakan ya ba da damar saka hannun jari a fannin ayyukan jinƙai, samar da ababen more rayuwa, da samar da tsaro.

 

Shugaban ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke na bai wa ƙananan hukumomi ’yancin cin gashin kan su, bayan ƙarar da Gwamnatin Tarayya ta shigar, yana da nufin ƙarfafa harkokin mulki a matakin ƙananan hukumomi da kuma samar da cigaba.

 

Shugaba Tinubu ya jaddada kuɗirin sa na ganin Nijeriyar da ba a bar wani ɗan ƙasa a baya ba a cikin talauci ko cuta wanda hakan na jawo mutuntawa a duniya.

 

Ya ce: “An fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na naira 70,000 a dukkan ma’aikatun Gwamnatin Tarayya, inda da yawa daga cikin gwamnatocin jihohi suka ƙudiri aniyar aiwatar da hakan. Sama da ɗalibai 46,000 ne ke cin gajiyar asusun ba da lamuni na ilimi na Nijeriya a faɗin manyan makarantu 59 da sama da naira biliyan 5. Kashi na farko na ma’aikatan gwamnati 500,000 ne za su ci gajiyar shirin bayar da lamuni na masu amfani da naira biliyan 100.

 

“Yayin da man fetur ya kasance babbar hanyar samun kuɗaɗen shiga ga Nijeriya, muna zuba jari sosai a wasu ɓangarori don bunƙasa tattalin arzikin mu don samun cigaba mai ɗorewa.

 

“Ƙaddamar da shirin Shugaban Ƙasa kan iskar gas (CNG) dabara ce don yin amfani da albarkatun iskar gas ɗin mu don rage tsadar sufuri da kusan kashi 60 da kuma samar da yanayi mai tsafta da lafiya ga ‘yan ƙasa. Wannan yunƙurin ya samar da kusan dala miliyan 200 na jarin kamfanoni masu zaman kan su a cikin shekara ɗaya da ta gabata.”

 

Ya ce kowane ɗaya daga cikin shirye-shiryen an tsara shi ne domin ya zama wani aiki da zai samar da cigaba mai ɗorewa a rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya.

 

Yayin da yake yaba wa kafafen yaɗa labarai kan sadaukar da kai ga gina ƙasa, musamman wajen tallafa wa dimokuraɗiyyar Nijeriya, Tinubu ya jaddada cewa ayyukan gwamnati da na kafafen yaɗa labarai na da alaƙa da juna, kuma dukkan su suna da matuƙar muhimmanci wajen amfanar da jama’a.

 

Ya ce: “Haka zalika, ya zama wajibi kafafen yaɗa labarai su riƙa tuntuɓar waɗanda aka zaɓa da waɗanda aka naɗa, da kuma tabbatar da cewa muna gudanar da ayyukan mu ta hanyar da za ta ƙarfafa dimokiraɗiyya – ba ta raunana ta ba. Wannan muhimmin aiki kuma dole ne a yi shi cikin mutunta juna da haɗin kai, ba wai ƙyama da adawa ba; wannan daidaitawar tana ba mu damar cimma manufofin gamayya da ke amfanar al’umma gaba ɗaya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

Next Post

Xi Ya Gana Da Shugaban Indonesia

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

8 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

9 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

11 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

12 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

13 hours ago
Next Post
Xi Ya Gana Da Shugaban Indonesia

Xi Ya Gana Da Shugaban Indonesia

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.