• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Yana Farfaɗowa Sannu A Hankali – Tinubu 

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Tattalin Arzikin Nijeriya Yana Farfaɗowa Sannu A Hankali – Tinubu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa, sannu a hankali tattalin arzikin Nijeriya na farfaɗowa, yana mai alaƙanta cigaban da aka samu da sauye-sauyen da gwamnatin sa ke aiwatarwa a sassa daban-daban.

 

Shugaban ya bayyana haka ne a garin Yenagoa na Jihar Bayelsa a ranar Alhamis a jawabin sa na buɗe babban taron shekara na Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE).

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje
  • An Kama Wasu Ƴansanda Kan Zargin Kisan Ɗalibin Jami’ar Kwara

Da yake magana ta bakin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, Shugaba Tinubu ya ce ya shafe watanni goma sha takwas da suka gabata yana kafa harsashin samar da Nijeriya mai arziki.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Ya ce: “Ina farin cikin sanar da ku cewa ta hanyar gyare-gyaren mu, muna ganin tattalin arzikin mu yana farfaɗowa. A yau, biyan ɗin bashin da muke yi da kuɗin shiga ya sauko sosai daga kusan kashi 100 zuwa kusan kashi 65.

 

“An shafe watanni goma sha takwas da suka gabata wajen aza harsashin wannan kyakkyawar manufa ta samar da cigaban Nijeriya.

 

“Wannan shi ne abin da Ajandar Sabunta Fata ke tattare da shi – wato sake farfaɗo da imani da fatan dukkan ‘yan Nijeriya kan yadda ƙasar su za ta bunƙasa da kuma samar da yanayin da zai bai wa kowa da kowa a cikin ta damar bunƙasa.

 

“Amma mun fahimci cewa akwai wasu manyan cikas da ke kan hanyar fito da ɗimbin abubuwan da Nijeriya ke da su. Kuma mun yi amfani da lokaci da kuzari kuma mun mai da hankali wajen magance waɗannan.

 

“Biyu daga cikin manyan abubuwan da suka fi muhimmanci sanannu ne a gare ku: tsarin tallafin man fetur wanda ya hana mu samun biliyoyin daloli a duk shekara da za a iya saka hannun jari da su a muhimman abubuwan more rayuwa, da tsarin musayar kuɗaɗen ƙasashen waje wanda za a iya amfani da shi ta hanyar da ba ta dace ba.”

 

Ya bayyana cewa sakamakon gyare-gyaren da aka yi, kuɗaɗen shiga na dukkan matakai uku na gwamnati – wato Tarayya, Jihohi, da Ƙananan Hukumomi – ya samu bunƙasa sosai, wanda hakan ya ba da damar saka hannun jari a fannin ayyukan jinƙai, samar da ababen more rayuwa, da samar da tsaro.

 

Shugaban ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke na bai wa ƙananan hukumomi ’yancin cin gashin kan su, bayan ƙarar da Gwamnatin Tarayya ta shigar, yana da nufin ƙarfafa harkokin mulki a matakin ƙananan hukumomi da kuma samar da cigaba.

 

Shugaba Tinubu ya jaddada kuɗirin sa na ganin Nijeriyar da ba a bar wani ɗan ƙasa a baya ba a cikin talauci ko cuta wanda hakan na jawo mutuntawa a duniya.

 

Ya ce: “An fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na naira 70,000 a dukkan ma’aikatun Gwamnatin Tarayya, inda da yawa daga cikin gwamnatocin jihohi suka ƙudiri aniyar aiwatar da hakan. Sama da ɗalibai 46,000 ne ke cin gajiyar asusun ba da lamuni na ilimi na Nijeriya a faɗin manyan makarantu 59 da sama da naira biliyan 5. Kashi na farko na ma’aikatan gwamnati 500,000 ne za su ci gajiyar shirin bayar da lamuni na masu amfani da naira biliyan 100.

 

“Yayin da man fetur ya kasance babbar hanyar samun kuɗaɗen shiga ga Nijeriya, muna zuba jari sosai a wasu ɓangarori don bunƙasa tattalin arzikin mu don samun cigaba mai ɗorewa.

 

“Ƙaddamar da shirin Shugaban Ƙasa kan iskar gas (CNG) dabara ce don yin amfani da albarkatun iskar gas ɗin mu don rage tsadar sufuri da kusan kashi 60 da kuma samar da yanayi mai tsafta da lafiya ga ‘yan ƙasa. Wannan yunƙurin ya samar da kusan dala miliyan 200 na jarin kamfanoni masu zaman kan su a cikin shekara ɗaya da ta gabata.”

 

Ya ce kowane ɗaya daga cikin shirye-shiryen an tsara shi ne domin ya zama wani aiki da zai samar da cigaba mai ɗorewa a rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya.

 

Yayin da yake yaba wa kafafen yaɗa labarai kan sadaukar da kai ga gina ƙasa, musamman wajen tallafa wa dimokuraɗiyyar Nijeriya, Tinubu ya jaddada cewa ayyukan gwamnati da na kafafen yaɗa labarai na da alaƙa da juna, kuma dukkan su suna da matuƙar muhimmanci wajen amfanar da jama’a.

 

Ya ce: “Haka zalika, ya zama wajibi kafafen yaɗa labarai su riƙa tuntuɓar waɗanda aka zaɓa da waɗanda aka naɗa, da kuma tabbatar da cewa muna gudanar da ayyukan mu ta hanyar da za ta ƙarfafa dimokiraɗiyya – ba ta raunana ta ba. Wannan muhimmin aiki kuma dole ne a yi shi cikin mutunta juna da haɗin kai, ba wai ƙyama da adawa ba; wannan daidaitawar tana ba mu damar cimma manufofin gamayya da ke amfanar al’umma gaba ɗaya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

Next Post

Xi Ya Gana Da Shugaban Indonesia

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

2 hours ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

3 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

3 hours ago
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Labarai

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

5 hours ago
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

7 hours ago
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 
Labarai

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

8 hours ago
Next Post
Xi Ya Gana Da Shugaban Indonesia

Xi Ya Gana Da Shugaban Indonesia

LABARAI MASU NASABA

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.