• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinkarar Sauyin Yanayi Na Bukatar Gaggauta Sauke Nauyin Da Ya Rataya A Wuyan Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Tinkarar Sauyin Yanayi Na Bukatar Gaggauta Sauke Nauyin Da Ya Rataya A Wuyan Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da aka tsawaita lokacin taron da kimanin sa’o’i 35, a sanyin safiyar ranar 24 ga wata agogon wurin, an rufe taron masu ruwa da tsaki na yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 29, wanda aka fi san shi da COP29, a birnin Baku, fadar mulkin kasar Azerbaijan, inda mahalarta taron suka cimma jerin daidaito ta fannin tinkarar sauyin yanayi.

 

Ba a cikin sauki aka yanke shawarwari a taron ba, inda aka fuskanci babban sabani tsakanin kasashe masu ci gaba da kuma kasashe masu tasowa ta fannin yawan kudin da za a samar na tinkarar sauyin yanayi. Da farkon farawa, kasashe masu ci gaba sun gabatar da manufar samar da dala biliyan 100 a kowace shekara, wanda ya samu rashin amincewa daga baki dayan kasashe masu tasowa. Daga karshe, sun yi alkawarin jagorantar samar da a kalla dala biliyan 300 a kowace shekara, don tallafawa kasashe masu tasowa wajen tinkarar matsalolin sauyin yanayi.

  • Yahaya Bello Ya Fada Komar EFCC, Zai Amsa Tambayoyi 
  • Mutum 1 Ya Rasu, An Ceto 14 Yayin Da ‘Yansanda Suka Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Katsina 

Duk da haka, kasashe masu tasowa na bukatar dala triliyan 1.3 don tinkarar tumbatsar ruwan teku, da fari, da ambaliya, da dai sauran matsalolin da sauyin yanayin duniya ke haifarwa, wanda akwai sauran babban gibi duk da dala biliyan 300 da aka yi alkawarin samarwa. Don haka, wakilin kasar Saliyo da ya halarci taron ya yi nuni da cewa, dala biliyan 300 bai kai rubu’i na kudaden da ake bukata ba, ba zai kai ga hana matsalolin sauyin yanayi ba. Kasashen Afirka sun yi bakin ciki da sakamakon da aka cimma, kuma kasashe masu ci gaba ba su da niyya wajen daidaita matsalar.

 

Labarai Masu Nasaba

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Ban da haka, a kan batun yadda za a samar da kudin da ake bukata, Amurka da kungiyar tarayyar Turai sun yi kokarin matsa wa kasashe da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa amma wadanda har yanzu kasashe masu tasowa ne, ciki har da kasar Sin, inda suka bukace su da su ma su samar da kudin. Sai dai hakan sam bai dace ba, akasarin matsalolin sauyin yanayi da ke addabar kasashen duniya sun samo asali ne daga yadda kasashe masu ci gaba suka shafe daruruwan shekaru suka bunkasa masana’antu tare da fitar da hayaki mai dumama yanayi masu yawan gaske. A hakika, bunkasuwar masana’antunsu ta tabbatar musu ci gaban tattalin arziki da kyautatar zaman al’umma, amma kuma kasashe masu tasowa ne suke dandana kudarsu dalilin matsalolin sauyin yanayi da hakan ya haifar. Don haka, kamata ya yi kasashe masu ci gaba su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu, kuma wannan shi ne dalilin da ya sa aka sanya “ana tare amma an sha bambam a fannin daukar alhaki” a matsayin muhimmiyar ka’idar da ake bi wajen yin shawarwarin sauyin yanayi karkashin MDD.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, har kullum, kasar Sin na aiwatar da manufar tinkarar sauyin yanayi da neman cimma burinta na rage fitar da iskar Carbon. Tun daga shekarar 2012, kasar Sin ta tabbatar da bunkasuwar tattalin arziki na sama da kaso 6% a kowace shekara bisa karuwar makamashin da take amfani na kimanin kaso 3% kawai, har ma yawan hayakin Carbon da ta fitar ya ragu da kaso 35%. Har wa yau, ya zuwa karshen watan Yunin bana, yawan wutar lantarki da kasar Sin ke iya samarwa ta makamashin dake iya sabuntawa ya kai KW biliyan 1.65, adadin da ya zarce rabin wutar lantarki da kasar ke iya samarwa baki daya. In an lura kuma, a yayin taron COP29 na bana, yawan motocin da ke aiki da lantarki da kasar Sin ta samar a shekara ya zarce miliyan 10, matakin da ya sanya ta zama kasa ta farko a duniya da yawan motocin lantarki da ta samar a shekara ya zarce miliyan 10. Ban da haka, kasar Sin tana kuma yawan aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa ta fannin tinkarar sauyin yanayi, inda kawo karshen watan Yunin bana, ta rattaba hannu a kan takardun hadin gwiwar tinkarar sauyin yanayi 52 tare da kasashe masu tasowa 42, don inganta kwarewarsu wajen tinkarar sauyin yanayi.

 

Kafin a kaddamar da taron COP29, kungiyar kula da yanayin duniya (WMO) ta fitar da wani rahoto, inda ta yi hasashen shekarar 2024 da muke ciki za ta iya kasancewa shekara mafi zafi tun bayan da aka fara samun bayanan yanayin duniya. A karshen watan da ya gabata, mummunar ambaliya ta afkawa kasar Spaniya, ambaliyar da ake kallonta a matsayin mafi muni a tarihin kasar. Sai kuma an yi ta fama da gobarar daji a Canada da kuma mahaukaciyar guguwa a kasar Amurka. Ko a Nijeriya, ambaliya da ta afkawa sassan kasar a bana ta haddasa mutuwar mutane sama da 300, tare da raba mutane sama da dubu 740 da muhallansu… Wadannan duka sun shaida mana cewa, tinkarar sauyin yanayi aiki ne dake gaban dan Adam baki daya, kuma babu kasar da za ta tsira ita kadai ba.

 

Tinkarar sauyin yanayi na bukatar gaggauta sauke nauyin da ya rataya a wuyan kasa da kasa. Muna kira ga kasashe masu ci gaba da su cika alkawarin da suka dauka na samar da dala miliyan 300 a kowace shekara don tallafawa kasashe masu tasowa tinkarar sauyin yanayi, kuma su karfafa niyyarsu da matakansu. A nasu bangaren kuma, kasashe masu tasowa kamata ya yi su yi iyakacin kokarinsu. Ya zama dole ‘yan Adam su hada kansu wajen tinkarar sauyin yanayi, sabo da duniya gida na bai daya ne gare mu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yahaya Bello Ya Fada Komar EFCC, Zai Amsa Tambayoyi 

Next Post

Tinubu Zai Tafi Faransa Don Ziyarar Aiki Ta Kwana Uku A Gobe Laraba

Related

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

1 day ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

2 days ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

5 days ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

1 week ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

2 weeks ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 weeks ago
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Tafi Faransa Don Ziyarar Aiki Ta Kwana Uku A Gobe Laraba

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.