• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

by Sani Anwar
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya bayyana cewa; ko kaɗan gwamnatin Tinubu ba ta shirya gudanar da sahihin zaɓe a 2027 ba.

Galadima ya bayyana haka ne, a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise. 

Ya ce, “Wannan gwamanatin, ko kaɗan ba ta shirya gudanar da sahihin zaɓe ba, kamar yadda suke ɓata jam’iyyu; hakan ne yake nuna cewa, ba sa ƙaunar adawa ko kaɗan, musamman idan lokacin zaɓe ya zo”. 

  • Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari.
  • Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

A cewar Galadima ana raɗe-raɗin cewa, shugaban ƙasar na shirin naɗa wani ɗan kama-karya a matsayin shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa. 

Galadima ya yi matuƙar gargaɗi ga wannan tare da cewa; yin hakan zai iya dagula zaman lafiyar ƙasar ko kuma haifar da wani yaƙin na Basasa. 

Labarai Masu Nasaba

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Ya ƙara da cewa, “Ina fatan hakan ba gaskiya ba ne, domin kuwa idan wannan mutum ya zama shugaban INEC, ko shakka babu; wannan gwamnati kai tsaye na gayyato yaƙin Basasa ne.”

Da yake mayar da martani a kan batutuwan da jam’iyyun siyasa suka fara yi na yaƙin neman zaɓe, ya zargi hukumar zaɓe ta ƙasa da gazawa waje aiwatar da dokokin yaƙin neman zaɓe.

“Wannan batu na yaƙin neman zaɓe kafin hukumar INEC ta ba shi dama, gwamnatin wancan lokacin ce ta fara yin hakan, wanda kuma hakan ke nuni da cewa; hukumar INEC ba za ta iya yin alƙalanci na gaskiya da adalci ba,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa; jam’iyyun adawa sun “Faɗa tarkon” APC ta hanyar shiga yaƙin neman zaɓe da wuri.

Har ila yau, a zaɓen cike gurbi na baya-bayan nan, Galadima ya yi watsi da nasarar da APC ta samu, inda ya yi misali da Jihar Kano da Zamfara, musamman ganin yadda jami’an tsaro suka tsorata masu kaɗa kuri’u”.

Ya ƙara da cewa, “Ba su ci zaɓe ko guda ɗaya ba, amma sun sanar a matsayin su ne waɗanda suka lashe zaɓen. A mazaɓar Bagwai da Shanono, mun samu ƙuri’a 16,000; yayin da APC ta samu ƙuri’a 5,000. A wata ƙaramar hukumar kuma, NNPP ta samu sama da ƙuri’a 5,700, yayin da APC kuma ta samu ƙuri’a 265 kacal.

“Sama da sojoji 30,000 aka kai Zamfara, domin aiwatar da zaɓukan mazaɓu biyar kacal. An yi wa mutane dukan tsiya, an nakasa wasu, an kori wasu, sannan a ƙarshe sun rubuta wa kansu sakamakon zaɓen tare kuma da bayyanawa.”      

 Dangane da irin ƙarfin da jam’iyyar NNPP ke da shi, Galadima ya bayyana cewa; Shugabanta Rabiu Musa Kwankwaso, ba shi da abokin karawa idan ana batu na tasiri a siyasance.

“Kwankwaso shi ne babban jigon siyasar Nijeriya, domin kuwa shi kaɗai ne, wanda tauraronsa yake haskawa; saboda haka, idan har za a yi zaɓe na gaskiya, shi ne mafi farin jini a Nijeriya,” in ji shi. 

Haka zalika, ya yi watsi da rahotannin da ke cewa; Kwankwaso ya gana da shugaba Bola Tinubu kwanan nan.

“Ƙarya ne batun cewa, Kwankwaso ya gana da Tinubu a Faris. Ai wannan cin fuska ne ma, ta yaya za ka yi wa wanda ya ayyana ka a matsayin maƙiyi aiki?” Ya ƙara da cewa, NNPP ta kori waɗanda suka yi iri wannan ta’asa ba tare da amincewar jam’iyyar ba. 

Dangane da ƙawancen siyasa kuma, Galadima ya ce; son kai a tsakanin ƴ an adawa, shi ne musabbabin hana haɗin kai a tsakaninsu.

“Zan so dukkaninmu mu haɗu mu ceci wannan ƙasa tamu baki-ɗaya, amma dukkaninmu, mun san wa da wa ya kamata a tsayar a Nijeriya, domin samun nasarar lashe zaɓe? 

Ya kuma nuna farin cikinsa da batun tattaunawar da aka samu rahoto cewa, ana yi tsakanin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour Party, inda ya bayyana cewa, “Idan za su iya haɗa kawunansu wuri guda, su fitar da mutum ɗaya; babu shakka ƙasa za ta ɗauki saiti, domin kuwa hakan zai kasance tamkar wata dabara ce ta fitar da mu daga cikin wannan ƙunci da muke ciki.” 

Da yake watsi da batun siyasar yanki da shiyya, Galadima ya ce; “Ban yarda da batun siyasar Arewa da Kudu ba. Mafi cancantar ɗan Nijeriya, ko daga ina ya fito, ko da kuwa daga mafi ƙanƙantar yare ne, shi ya kamata a zaɓa.” 

Galadima ya kuma goyi bayan yawaitar jam’iyyu, yana mai cewa; ko kaɗan bai kyautu a tauye yawansu a Nijeriya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GaladimaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Next Post

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

Related

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU
Manyan Labarai

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

7 minutes ago
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Manyan Labarai

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

16 hours ago
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli
Manyan Labarai

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

23 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

1 day ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

1 day ago
Next Post
Tinubu

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

September 21, 2025
Tinubu

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

September 21, 2025
Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

September 21, 2025
Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.