• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sababbin naɗe-naɗe takwas na shugabannin hukumomin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Kakakin Shugaban Ƙasa, Mista Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Alhamis.

  • ‘Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya – Minista
  • Za Mu Dasa Wa ‘Yan Nijeriya Dabi’ar Gaskata Kalaman Shugabanni A Zukatansu – Minista

Sanarwar ta bayyana cewa an naɗa Mista Lanre Issa-Onilu a matsayin Shugaban Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA); Alhaji Salihu Abdulhamid Dembos a matsayin Shugaban Gidan Talbijin na Nijeriya (NTA), da Dakta Muhammad Bulama a matsayin Darakta-Janar na Hukumar Rediyon Tarayya na Nijeriya (FRCN).

Ita kuma Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), an naɗa mata Mista Charles Ebuebu a matsayin shugaba, yayin da aka naɗa Alhaji Jibrin Baba Ndace a matsayin Shugaban gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON).

Haka kuma an naɗa Dakta Lekan Fadolapo matsayin Shugaban Hukumar Kula da Tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), da Malam Ali M. Ali a matsayin Shugaban Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), sai Hukumar Kula da Gidajen Jaridu ta Ƙasa (NPC) wadda aka naɗa Dili Ezughah matsayin shugaban ta.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shugaba Tinubu ya hori waɗannan sababbin shugabannin da cewa su ƙirƙiro tare da bijiro da sababbin fasahohi da damarmakin da ‘yan Nijeriya za su amfana, ta yadda za a ci moriyar canji a hukumomin domin ƙarfafa haɗin kai a ƙasar nan.

Ya ce ta haka za su bayar da gagarumar gudunmawar ɗaukaka Nijeriya har ta yi goyayya da manyan ƙasashen duniya.

Sanarwar ta ce naɗin nasu ya fara aiki nan take.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NANNOANTA
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Dakatar Da Shugaban Jam’iyyar APC A Jigawa Kan Zargin Fyade

Next Post

Kotun Koli Ta Naɗa Alkalai 7 Da Za Su Saurari Daukaka Karar Atiku, Obi A Kan Tinubu

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

2 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

3 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

5 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

6 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

9 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

10 hours ago
Next Post
Zaben 2023: Atiku Da Obi Sun Shigar Da Kara Ta Kalubalantar Nasarar Tinubu

Kotun Koli Ta Naɗa Alkalai 7 Da Za Su Saurari Daukaka Karar Atiku, Obi A Kan Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.