ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Koli Ta Naɗa Alkalai 7 Da Za Su Saurari Daukaka Karar Atiku, Obi A Kan Tinubu

by Abubakar Abba
3 years ago
Koli

Kotun koli ta kaddamar da alkalai bakwai da za su saurari koken da ‘yan takarar shugaban kasa suka shigar a gabanta na kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabirairun 2023.

Bugu da kari, an gabatar da kwafi ga masu karar Atiku Abubakar, dan takakar shugaban kasa na jam’iyyar PDP da na jam’iyya LP Peter Obi da kuma Chichi Ojei ta jam’iyyar APM.

  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai
  • An Dakatar Da Shugaban Jam’iyyar APC A Jigawa Kan Zargin Fyade

Magatartar kotun, Zainab M. Garba wadda ta rattaba hannu a kwafin ta bayyana cewa, bisa sashen doka ta da ta 1(2) na kotun ta shekarar 1985 da aka sabunta, ya wajaba a bai wa masu karar kwafin.

ADVERTISEMENT

Kazalika, jerin sunyayen alkalan su ne, Musa Dattijo Muhammad, Uwani Musa Abba Aji, Lawal Garba, Helen M. Ogunwumiju, I.N. Saulawa, Tijjani Abubakar da kuma Emmanuel Agim.

Bugu da kari, Atiku cikin takardar daukaka karar da ya gabatarwa da kotun ya ce, kotun sauraron karar zaben ta yi kuskure akan fatalin da ta yi da karar da ya gabatar mata, akan gazawarsa na tabbatar wa da kotun hujja akan zargin tafka magudi a zaben shugaban kasa, na samun kuri’u kashi 25 a birnin tarayyar Abuja da kin biyan diyyar dala 60,000 da kuma gazawar INEC na tura sakamakon zaben da aka karbo daga mazabun da aka jefa kuri’u zuwa a cikin na’urar BVAS, kamar yadda doka ta tanadar.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kazalika, bababan Lauya (SAN) Chris Uche da ke mai tsaya wa Atiku a takardar da ya gabatar wa da kotun ya kuma gabatar wa da kotun zargin shedar kammala makaranta na Tinubu, bisa cewa na bogi ne.

Bugu da kari, a bangaren Obi kuwa yana jayayya ne akan yadda kotun sauraron kararrakin zaben ta ki amincewa da samun nasararsa a mazabu 18,088.

Ita kuwa Ojei ta jam’iyyar APM, a nata korafin ta nuna jayayya ne akan Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima kan cewa, a soke zabensu.

Sai dai, martanin da Tinubu ya mayar ta hanyar babban Lauyansa Wole Olanipekun (SAN) mai tsayawa ya bukaci kotun da dauki koken Atiku a matsayin cin mutuncin kotu.

Kazalika, Tinubu ya danganta korafin Obi matsayin mara tushe da hujja.

Koli
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
An Sace Masu Yi Wa Kasa Hidima 8 Da Direba A Zamfara

NYSC Ta Yi Jimami Kan Kisan ‘Yar Hidimar Kasa A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.