• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Tafi Faransa A Sabon Jirgin Da Aka Saya Masa

by Sadiq
11 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Tafi Faransa A Sabon Jirgin Da Aka Saya Masa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya tafi Faransa a sabon jirgin Airbus A330 da aka saya masa a cewar fadar shugaban kasa.

Jirgin ya maye gurbin tsohon da shugabannin Najeriya suka kwashe shekaru 19 ana amfani da shi in ji Kakakin Tinubu Bayo Onanuga.

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Karuwar Zargin Cin Zarafi A Rundunar Sojojin Amurka
  • Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Vietnam

“Wannan sabon jirgi da aka sayo a farashi mai rahusa, ya sa Najeriya za ta kauce wa kashe miliyoyin daloli wajen gyara da sayen mai a kowace shekara.” Onanuga ya ce a wani sako da ya wallafa a shafin Twitter a ranar Litinin.

Tun a zamanin tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo ake amfani da tsohon jirgin a cewar shi.

Maye gurbin tsohon jirgin mai lamba B737 – 700 (BBJ) ya biyo bayan zaman jin bahasi da majalisar dokokin Najeriya ta yi kan lafiyar jirgin da kuma kudin gyaransa, “musamman bayan da ya lalace yayin wata tafiya da aka yi da shi zuwa Saudiyya.”

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Sabon jirgin ya iso Abuja ne, daren ranar Lahadi, bayan kamfanin China da ya sa kotu ta kwace shi, ya amince ya saki guda daya da zai kai shugaba Tinubu Faransa.

Jirgin kirar 330 na daga cikin kadarorin wani attajirin da ke harkar mai ya mika shi ga bankin Jamus, a matsayin jinginar karbar lamuni, daga bisani kuma aka sayar da shi.

Bayanai sun ce wani kamfanin sufurin jiragen Amurka da ake kira L&L da ke Miami Florida ne, ya jagoranci yarjejeniyar sayar wa Nijeriya jirgin a kan sama da dala miliyan 100.

Wasu rahotanni sun bayyana cewar Nijeriya ta samu jirgin a farashi mai sauki domin a yanzu farashinsa ya kai Dala miliyan 600.

Kasaitaccen jirgin na alfarma yanzu ya zama jirgin shugaban kasa da ake kira ‘Nigeria Air Force One’ mai lamba 5N-NGA.

Wata majiya daga fadar shugaban kasa, ta ce sabon jirgin ya ci kudinsa saboda kayan alatun da ke ciki da kuma inagancinsa la’akari da girma da kuma kimar shugaban Nijeriya a idon duniya.

A baya dai an tafka mahawara a kan muhimmancin sauyawa shugaban kasa jirgi, ya yin da babu wani bayani daga fadar shugaban kasa dangane da wannan ciniki.

A baya’yan Nijeriya sun bayyana bacin ransu dangane da bukatar sayen sabon jirgin da Tinubu ya yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jirgin SamaJirgin Shugaban KasaNigeria Airforce OneTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NNPC Ba Ya Biyan Tallafin Man Fetur – Ajiya

Next Post

NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

5 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

6 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

10 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

11 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

13 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

13 hours ago
Next Post
NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.