ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Tura Badaru Neja Kan Sace Dalibai Sama da 200

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
Makarantar St. Mary, Neja

Makarantar St. Mary, Neja

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Shugaban kasa Bola Tinubu ya umarci Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar, da ya tafi zuwa jihar Neja domin jagorantar ƙoƙarin ceto ɗalibai fiye da 200 da ’yan bindiga suka sace a makarantar St. Mary da ke garin Papiri. Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana haka a shirin Ra’ayi Riga na BBC Hausa, inda ya ce wannan mataki na cikin hanzarin gwamnati na ganin an kubutar da dukkan waɗanda aka yi garkuwa da su.

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) ta tabbatar da cewa mutane 227 ne aka sace, ciki har da ɗalibai 215 da malamai 12. Shugaban CAN a Neja, Rev. Bulus Dauwa Yohanna, ya ce harin ya jefa al’ummar yankin cikin firgici, yayin da maharan suka shiga makarantar da tsakar daren Alhamis, suka harbe maigadi sannan suka yi awon gaba da ɗaliban firamare da sakandaren makarantar.

  • Muna Bukatar Gudunmawar Addu’o’in ‘Yan Nijeriya Don Yaki Da Matsalar Tsaro — Badaru
  • Badaru Na Da Kwarewar Jagorantar Ma’aikatar Tsaro – ANA

Gwamnatin jihar Neja ta bayyana cewa ta riga ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun yankin saboda barazanar tsaro, amma makarantar St. Mary ta buɗe ba tare da izini ko sanarwa ga hukumomi ba. Wannan ya faru ne kasa da sati guda bayan sace dalibai mata 25 a makarantar sakandaren ’yanmata da ke Maga, jihar Kebbi.

ADVERTISEMENT

A halin da ake ciki, gwamnatin tarayya ta ce ta baza jami’an tsaro domin ceto dukkan ɗaliban da aka sace a Neja da Kebbi. Karamin Ministan Tsaro Bello Matawalle ya ce kamar yadda aka tura shi Kebbi, haka ma Babban Ministan Tsaro Muhammad Badaru zai isa Neja don sa ido kai tsaye kan aikin kubutarwa da tabbatar da komawar daliban zuwa iyalansu lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
kiwon kaji

Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Sa Kajin Gidan Gonar Da Za Su Fara Yin Kwai A Keji

LABARAI MASU NASABA

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.