ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Sa Kajin Gidan Gonar Da Za Su Fara Yin Kwai A Keji

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
kiwon kaji

Wani kwararre a fannin kiwon kajin gidan gona, Dakta James Baba Wageti, ya bayyana cewa;  akasarin wadanda suke kiwon kajin gidan gona, don samun riba, na tabka kuskure a matakan farko na gudanar da kiwon; wanda hakan ya sa ba sa iya samun riba mai yawa.

James, wanda ke da kwarewa a fannin ta kusan kimanin shekara 31, ya zayyano kura-kuran da wasu masu kiwon ke yi.

  • Ribadu Ya Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Amurka Kan Zargin Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla
  • Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho

Kazalika, ya kuma bayar da shawarar da ta kamata su bi, wajen kaucewa yin kura-kuran, mussaman a lokacin da ya fi dacewa, su sauya kajinsu na gidan gona da ke shirin fara yin kwai.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa, a bisa ka’ida, kamata ya yi masu kiwon su sauya masu waje, ko kuma sanya su a cikin keji daga tsakanin mako13 zuwa 15.

Ya kara da cewa, yin amfani da wannan tsarin, na taimaka wa kajin na saba wa da wuri da kuma kara samun kwai mai tarin yawa.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ya ci gaba da cewa, rashin bin ka’idar; na iya jawo masu yin asara tare kuma da shafar lafiyar kajin.

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; nau’in kajin gidan gona, kamar na ‘Isa Brown’, akasari suna kai wa girman daga kashi 75 zuwa kashi 95 ba su kammala girmansu ne, wanda a lokacin nauyinsu ya kai zuwa mako 12.

“A daidai mako na 16, lokaci ne kajin ke samun sauyin da zai ba su damar fara yin kwan tare kuma da samun karfin jikinsu,” in ji kwararren.

Lokacin Da Ya Kamata A Sauyawa Kajin Wajen Da Za Su Yi Kwai:

Kwararen ya bayar da shawara kan lokacin da ya dace a sauyawa kajin wajen da za su fara yin kwan, wanda ya sanar da cewa; ya kamata hakan ya kasance a tsakanin mako hudu ko akalla mako biyu, kafin su fara yin kwan.

Ya ce, ‘yar wannan tazarar da ake samu, za ta bai wa kajin damar sabawa da sabon wurin kwannan da aka sauya musu da tsarin cin abincinsu da kuma rage musu wahalar da suka fuskanta a yayin kwashe su zuwa sabon wajen tare kuma da kare su daga rage nauyin jikinsu.

“A bisa kwarewar da nake da ita a fannin har ta tsawon shekara 31, kajin gidan gonar da aka sauyawa waje, nauyinsu na raguwa zuwa kashi 10 a cikin 100 ko sama da haka, wanda hakan ke taimaka musu murnurewa kafin su fara yin kwan,” a cewarsa.

Matsalolin Da Ke Afkuwa Na Sauya Musu Bayan Mako Na 16:

Sauya musu waje a cikin mako na 16 ko ga haka, zai iya lalata inda kajin ke ajiye da kwansu tare kuma da shafar karfin jikinsu. Kazalika, ya kara da cewa; hakan zai kuma iya yi wa kwanduwar kwan illa da kuma shafar kwanciyar kwanduwar kwan.

Shawara Ga Masu Kiwon Kajin Gidan Gona:

Kwararren ya sanar da cewa, ya kamata masu kiwon su tabbatar sun sanya su a keji ko kuma sun sauya musu wajen a tsakanin 13 zuwa 15 yadda jikinsu zai kasance a daidai kashi 85, bayan sauya musu wajen.

Ya kara da cewa, su kuma tabbatar da cewa; nauyinsu ya kai kilo 1.35 a yayin da suke mako na 16 ko kuma nauyinsu ya kai kilo 1.5 a yayin da suke mako na 18.

A cewarsa, ana kuma bukatar su samar musu daidaito na abinci mai gina jiki da kuma sanya ido kan yanayin haske a lokacin da za a sauya musu wajen.

Mako na 18 Zuwa Na 43 Su Ne Lokuta Mafi Tsanani: Dakta Wageti ya alakanta mako na 18 zuwa na 42 a matsayin lokacin da ya kamata mai kiwon Kajin gidan gona ya tabbatar yana sanya ido matuka duba da cewa; lokuta ne da suka kasance mafi tsanani da ke nuna lokacin fara yin kwan kajin gidan gona.

Ya ce, a tsakanin wannan lokacin ne, makin da nauyin kajin ke karuwa daga kilo1.5 zuwa kimanin daya zuwa kilo 2.0, kuma lokaci ne da suke shirin fara yin kwai tare kuma da karuwar girman kwansu zuwa akalla daga kilo 40 zuwa kilo 60.

gidan gona
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
gidan gona
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Matar Sarkin Suleja Mai Martaba Malam Muhammad Awwal Ibrahim Ta Rasu

Matar Sarkin Suleja Mai Martaba Malam Muhammad Awwal Ibrahim Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.