• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bola Ahmed Tinubu, zababben shugaban kasa ya bayyana cewa ‘yan fashi, ta’addanci da kashe-kashen hankali bai kamata su zama wurin zama a Nijeriya ba.

Ya bayyana ra’ayinsa ne kan hare-haren da ‘yan bindiga da mahara suka kai a karamar hukumar Maru a Jihar Zamfara a karshen mako da kuma garin Maigari da ke karamar hukumar Rimin Gado a Jihar Kano.

  • Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku
  • Ba Za Mu Bari NNPP Ta Yi Magudin Zabe A Kano Ba —Gwamnatin Kano

Tinubu ya bayyana cewa an kashe jami’in ‘yan sanda da dan banga a harin da ‘yan bindiga suka kai a Zamfara.

“A harin na Kano, ‘yan bindiga sun kutsa gidan wani basarake inda suka harbe shi har lahira,” in ji zababben shugaban kasar.

Ya kara da cewa harin da aka kai garin Maru bayan an samu zaman lafiya a Zamfara, ya kara da cewa akwai bukatar a kara kaimi domin murkushe ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

“A matsayinmu na kasa dole ne mu hada kai domin mu fatattaki wadannan ‘yan ta’addanci gaba daya. Kashe-kashen rashin hankali da ta’asa irin wannan bai kamata su kasance a kasarmu ba,” in ji shi.

Ya jajantawa Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Mista Usman Baba, da gwamnatin Zamfara da iyalan jami’an tsaron da abin ya shafa game da rasuwar.

Tinubu ya kuma bukaci a gudanar da bincike kan kisan Hakimin Maigari a Jihar Kano, wanda shi ne mahaifin Shugaban karamar Hukumar Rimin Gado, Mista Munir Maigari.

Ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban karamar hukumar, da gwamnatin Jihar Kano da kuma iyalan marigayin bisa mummunan kisan da aka yi wa shugaban al’umma.

A cikin sakon ta’aziyya daban-daban, zababben shugaban kasar ya jajanta wa fitaccen malamin nan Sheikh Ahmad Gumi da ya rasa mahaifiyarsa da kuma iyalan marigayi Janar Sani Abacha bisa rasuwar dansu Abdullahi.

“Akwai kuna rabuwa da masoyi komai yanayi da shekaru.

“Ba za mu iya tambayar Allah ba, sai dai kawai mu yi addu’a Allah Ta’ala ya jikansu, ya kuma ba mu karfin jure wa rashinsu,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Allah WadaiHarikanoTinubuZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

Next Post

Zaben Gwamnoni: ‘Yan Sanda Za Su Hukunta Masu Yada Labaran Karya A Legas

Related

Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

6 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

11 hours ago
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta
Manyan Labarai

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

12 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

2 days ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

2 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Damfara Da Katin Cirar Kudi 10 A Adamawa 

Zaben Gwamnoni: 'Yan Sanda Za Su Hukunta Masu Yada Labaran Karya A Legas

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.