ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

by Naziru Adam Ibrahim
3 days ago
Tinubu

Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun sanar da shirin karɓar daftarin kasafin kuɗin shekarar 2026 a hukumance, yayin zaman haɗin gwuiwa da aka shirya gudanarwa a ranar Juma’a.

Sanarwar na ƙunshe ne a wata wasiƙa da Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya karanta a zauren majalisar a ranar Alhamis, inda shi ma Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta makamanciyar wasiƙa a zauren Majalisar Dattawa.

  • Kamfanonin Sin Da Zimbabwe Za Su Yi Hadin Gwiwa Wajen Kera Na’urorin Wutar Lantarki
  • Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Sun Jima Suna Kitsa Karairayi

A cewar wasiƙar, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, zai gabatar da daftarin kasafin shekarar 2026 da misalin ƙarfe 2 na ranar Juma’a, tare da sa ran zaman zai koma zauren Majalisar Wakilai da misalin ƙarfe 1:45 na rana.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangare kuma, Majalisar Dattawa ta karɓi wasiƙu biyu daban-daban daga Shugaban Ƙasa Tinubu, inda yake neman tabbatar da naɗin shugabannin hukumomin kula da harkokin man fetur, bisa tanade-tanaden Dokar Masana’antar Man Fetur ta 2021 (PIA).

A wasiƙar farko, Shugaban Ƙasa ya nemi Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin Injiniya Saidu Muhammad, a matsayin Babban Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur ta ƙasa (NMDPRA), bisa sashe na 41(6) na PIA 2021, yana mai bayyana cewa wannan naɗi ya biyo bayan murabus ɗin tsohon Babban Shugaban hukumar.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Ya jaddada buƙatar kaucewa giɓi a shugabancin hukumar, duba da rawar da muhimmancinta wajen kula da ayyukan da suka jiɓanci man fetur da izinin zirga-zirgarsa a jiragen ruwa.

A wasiƙa ta biyu kuma, Shugaban Ƙasa ya nemi tabbatar da naɗin Mista Oritsemanori Sewa Inyosa, a matsayin Babban Shugaban Hukumar Kula da bayar da lasisin dakon man fetur zuwa ƙasar nan (NUPRC), bisa sashe na 11(3) na Dokar PIA 2021, inda dukkan naɗe-naɗen aka miƙa su ga Kwamitin Majalisa domin gaggauta duba su tare da yiwuwar amincewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.